An tabbatar da mutuwar mutum guda, yayin da sama da mutum 30 suka ɓace sakamakon wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a ƙauyen Malamawar ‘Yan Dutse da ke Ƙaramar Hukumar Ringim a Jihar Jigawa.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Lahadi lokacin da kwale-kwalen, wanda ke ɗauke da manoma da ma’aikata ciki har da mata, ke dawowa daga gonaki zuwa ƙauyensu.
Wata majiya daga ƙauyen ta bayyana cewa fiye da mutane 40 ne ke cikin kwale-kwalen lokacin da hatsarin ya faru.
Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, Daraktan Tsare-tsare na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA) ya ce ana ci gaba da gudanar da aikin ceto tare da haɗin gwiwar masu ceto na ruwa na yankin, jami’an SEMA da sauran hukumomin da abin ya shafa.
Ya ce, “Dukkan jami’an da abin ya shafa suna aiki ba dare ba rana domin tantance adadin mutanen da aka ceto da kuma waɗanda har yanzu ake nema.”
A halin da ake ciki, Shugaban Kwamitin Ba da Agajin Gaggawa na Ƙaramar Hukumar Ringim, Malam Habibu Dauda, ya yi kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu, tare da gujewa yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da sahihancinsu ba har sai hukumomin da suka dace sun fitar da cikakken bayani kan lamarin.














