Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf, ya ce gwamnatinsa ta cika kashi 90 cikin 100 na alkawuran da ta ɗauka wa al’ummar jihar cikin shekaru uku da ta yi tana mulki.
Gwamnan ya bayyana hakan ne ranar Asabar yayin da yake karbar Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa ziyarar gaisuwar Sallah a gidan gwamnati da ke Kano.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Darakta Janar na Yada Labarai da Hulda da Jama’a na gidan gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Asabar.
Yusuf ya ce gwamnatinsa ta ci gaba da jajircewa wajen samar da ribar dimokuradiyya ta hanyar manufofi masu amfani ga jama’a da ayyukan ci gaba a muhimman bangarorin tattalin arziki.
A cewarsa, an samu gagarumin ci gaba a bangarorin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, noma, samar da ruwa, tallafa wa matasa da kuma bunkasa tattalin arziki.
Gwamnan ya ce an aiwatar da wadannan shirye-shirye ne domin inganta rayuwar al’umma tare da mayar da jihar Kano kan turbar ci gaba mai dorewa.















Discussion about this post