ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago

Jami’an Rundunar Ƴansanda na Sashen Zone 2 (Nigeria Police Force) sun bankaɗo wata babbar ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi a Jihar Legas, inda suka ƙwato miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta kai kimanin Naira biliyan 7.8 tare da kama wasu mutane da ake zargi, ciki har da wanda ake zaton jagoran ƙungiyar ne, Eke Henry Ifeanyi.

An gudanar da aikin ne ta hannun jami’an Special Protection Unit (SPU) tare da haɗin gwiwar jami’an bincike na sassa daban-daban, bayan shafe watanni ana bibiyar motsin waɗanda ake zargi bisa bayanan sirri da aka tattara daga hedikwatar Zone 2.

Sumamen ya gudana ne a wani gida da ke cikin wani rukunin gidaje a Mende, Maryland a Legas, inda aka gano buhunan miyagun ƙwayoyi da ake zargin “Canadian Loud” da aka ajiye a gidan wanda ake zaton jagoran ƙungiyar.

ADVERTISEMENT

Da yake magana da manema labarai a wurin sumamen a ranar Asabar, Mataimakin Sufeto-Janar na Ƴansanda na Zone 2, AIG Olohundare Jimoh, ya bayyana cewa an kama wanda ake zargi a ranar 19 ga Mayu bayan shafe makonni ana sa ido kan motsinsa ta hanyar jami’an tsaro.

A cewarsa, an gudanar da aikin ne da goyon baya da shawarwari daga Sufeto-Janar na Ƴansanda, IGP Olatunji Disu, tare da haɗin gwiwar jami’an SPU da na sassan bincike na rundunar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Jimoh ya bayyana cewa yayin aikin, wanda ake zargin ya yi ƙoƙarin bayar da cin hanci na Naira miliyan 500 ga kwamandan SPU domin ya dakatar da aikin, ya kuma ba shi damar tuntuɓar abokan hulɗarsa su tafi da kayan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce an ƙi wannan tayin nan take, kuma an rubuta shi a matsayin hujja domin ci gaba da bincike.

“Wanda ake zargin ya bayar da Naira miliyan 500 ga kwamandan SPU domin ya sa tawagar ta ja baya, ya kuma ba shi damar kiran abokan aikinsa su tafi da kayan. An ƙi karɓar tayin nan take kuma an rubuta shi yadda ya kamata domin bincike,” in ji shi.

AIG ɗin ya bayyana wannan nasara a matsayin wani abin da ke nuna sabunta ƙwarewa da ƙa’idar aiki mai kyau da ake ƙoƙarin dasawa a cikin rundunar ƴansanda a ƙarƙashin sabon tsarin aikin tsaro.

Ya ce nasarar aikin ta nuna muhimmancin amfani da sassa na musamman na ƴansanda tare da jami’an bincike na unguwanni wajen yaƙar manyan laifuka.

Ya bayyana cewa: “An samu nasarar kame lamarin cikin gaggawa, inda Special Protection Unit ta haɗa kai da tawagogin bincike na unguwanni wajen kulle wurin da hana fasa guduwa ko shafar shaidun laifi.

“Aikin ya samo asali ne daga bayanan sirri, bayan shafe watanni ana bin diddigi da sa ido ta fasaha kafin a kai samamen.

“Ƙin karɓar cin hancin nan take da kuma rubuta shi yadda ya dace yana nuna ƙa’idar aiki da ake sa ran duk wani jami’i a matakin yanki ya bi,” in ji Jimoh.

Da yake mayar da martani, Sufeto-Janar na Ƴansandan Nijeriya, IGP Olatunji Disu, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, yana cewa nasarar ta tabbatar da fa’idar sake tura jami’ai zuwa sassa da ofisoshi a jihohin Legas da Ogun.

Ya ce: “Aikin ƴansanda dole ya kasance kusa da jama’a, kuma sassanmu na musamman dole su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da na unguwanni.

“Ƙwarewar da kwamandan SPU ya nuna ta hanyar ƙin karɓar cin hanci na Naira miliyan 500 da bin ƙa’ida yadda ya dace ita ce abin da muke so. Wannan yana nuna cewa idan aka tura jami’ai masu ƙwazo a matakin ƙasa, za a samu sakamako kuma amincewar jama’a za ta ƙaru,” in ji shi.

Hukumar ƴansanda ta ce an tattara kayayyakin da aka ƙwato a matsayin hujja, kuma za a gabatar da su a kotu. A halin yanzu, waɗanda ake zargi suna hannun hukuma yayin da bincike ke ci gaba domin gano sauran mambobin ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
2027: Fatanmu Mayar Da Nijeriya Wuri Mafi Alheri Ga Kowa – Kwankwaso

2027: Kwankwaso Zai Kasance Cikakken Abokin Tafiyar Da Gwamnati, Ba 'Safaya Taya' Ba – Obi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.