Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sanya hannu kan wata yarjejeniya da gwamnatin Habasha domin mayar da fursunonin Nijeriya sama da 100 da ke zaman hukunci a gidajen yari na kasar Habasha zuwa Nijeriya.
Ministar Harkokin Waje, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ce ta bayyana hakan a wani sako da ta wallafa a shafinta na X ranar Laraba.
Ta ce an sanya hannu kan yarjejeniyar ne tare da Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, domin sauƙaƙa dawo da ’yan Nijeriya da ke tsare a gidajen yarin Kaliti da Aba Samuel da ke Habasha.
A cewarta: “Ina Addis Ababa domin sanya hannu kan wata muhimmiyar yarjejeniya tare da gwamnatin Habasha, tare da AGF, Mai Girma Lateef Fagbemi, domin mayar da fursunonin Nijeriya sama da 100 da ke tsare a gidajen yarinsu, musamman a gidajen fursuna na Kaliti da Aba Samuel, zuwa Nijeriya.”
Ta bayyana cewa yarjejeniyar na da nufin bai wa waɗannan ’yan Nijeriya damar ci gaba da zaman hukuncinsu a cikin ƙasarsu, kusa da iyalansu da kuma a ƙarƙashin tsarin gyaran hali na Nijeriya.














Discussion about this post