ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Ta Zama Abokiyar Huldar BRICS

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
BRICS

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

A yayin gudanar da aikinta na shugabancin karba-karba na BRICS, gwamnatin Brazil ta sanar a ranar 17 ga Janairun 2025, da amincewa da Najeriya a matsayin abokiyar hadin gwiwar kungiyar ta BRICS. Hakan na nufin Najeriya ta zama kasa ta tara na abokan huldar BRICS, tare da kasashen Belarus, Bolivia, Cuba, Kazakhstan, Malaysia, Thailand, Uganda, da Uzbekistan. Wannan sabon tsarin da aka kirkiro a taron kolin BRICS karo na 16 a Kazan a watan Oktoban 2024 na taka rawar gani wajen karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa da kuma sake fasalin tsarin mulkin duniya. A halin yanzu BRICS tana da cikakkun mambobi 10 da suka hada da Brazil, Rasha, Indiya, Sin, Afirka ta Kudu, Masar, Habasha, Indonesiya, Iran, Hadaddiyar Daular Larabawa yayin da wasu kasashe da dama suke kan hanyarsu ta shiga kungiyar. Kasancewar cikakken mamba na kungiyar na nufin samun damar inganta mu’amalar hada-hadar kudi da sauran kasashe mambobi da samun garkuwa daga mamayar kasashen yammacin duniya, tare da samun damar shiga tsarin manufofi da kudurorin kungiyar wadanda suka ginu a kan hadin gwiwar mutunta juna kuma a gudu tare don a tsira tare.

A matsayinta na abokiyar huldar kungiyar, Najeriya na iya amfani da damar wajen rage dogaro da tasirin dalar Amurka a harkokin da suka shafi hada-hadar kudi tsakaninta da sauran kasashe tare da karfafa yin kasuwanci da kudinta. Hakan kuma zai iya taimaka mata wajen magance matsalolin da ake fuskanta na saye da sayar da kayayyaki, wadanda ke ci gaba da zama manyan ginshikai a cikin matsalar tattalin arzikin kasar. Har ila yau, duk da cewa Najeriya ba cikakkiyar mamba ba ce, za ta iya samun damar samun kudade bisa wasu sharudda na musamman don gudanar da ayyukan samar da ababen more rayuwa da ayyukan raya kasa ta hanyar Sabon Bankin Raya Kasa (NBD) da Contingent Reserve Arrangement (CRA). A cewar wani rahoton Majalisar Kula da Huldar Kasashen Waje (CFR) da aka wallafa a watan Disamba, daya daga cikin manyan manufofin BRICS shi ne yin ayyukan da za su maye gurbin bukatuwar mambobinta zuwa ga Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF). Mambobin BRICS na fatan cewa wannan tsarin ba da lamuni na iya karfafa hadin gwiwar kasashe masu tasowa da kuma rage dogaro ga hanyoyin samar da kudade na gargajiya. (Mohammed Yahaya)

BRICS
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos
BRICS
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa
  • Sulaiman
    An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”
  • Sulaiman
    Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
  • Sulaiman
    Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”
Daga Birnin Sin

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos
Daga Birnin Sin

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

June 5, 2026
Next Post
Sin A Shirye Take Ta Shawo Kan Sabani Tare Da Sabuwar Gwamnatin Amurka

Sin A Shirye Take Ta Shawo Kan Sabani Tare Da Sabuwar Gwamnatin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

June 5, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

June 5, 2026
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

June 5, 2026
Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

June 5, 2026
GORON JUMA’A 17-04-2026

Goron Juma’a

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.