Bisa gayyatar babban sakataren jam’iyyar ’yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kuma shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong-un, babban sakataren jam’iyyar kwaminis ta Sin JKS, kuma shugaban kasa Xi Jinping, ya gudanar da ziyarar aiki a Koriya ta Arewa daga ranar 8 zuwa 9 ga watan Yunin nan.
A yayin ziyarar, manyan shugabannin biyu sun shirya babban tsari bisa hangen nesa, dangane da dangantakar Sin da Koriya ta Arewa a sabon zamani, kuma sun amince da cewa, ya kamata a ciyar da dangantakar Sin da Koriya ta Arewa gaba zuwa babban matsayi mai cike da hangen nesa, bisa yanayin zamanin da muke ciki, da dogaro da makomar tsarin gurguzu.
Domin cimma wannan fa’ida bisa la’akari da ci gaban dangantakar jam’iyyu da kasashen biyu a dogon lokaci da kuma yanayin zamani, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda hudu, wato bukatar “Nacewa ga jagorancin manyan tsare-tsaren tuntubar shugabanni, don karfafa tushen amincewar siyasa” da “Nacewa ga burin amfanar da jama’a, don inganta hadin gwiwa mai amfani” da “Nacewa ga dorawa kan abota, don karfafa hadin kan jama’a”, kana da “Nacewa ga manufar adalci da gaskiya, don inganta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare”. Wadannan shawarwari sun kasance mataki da zai saita taswira da alkiblar ci gaban dangantakar Sin da Koriya ta Arewa a sabon zamani. (Amina Xu)














Discussion about this post