ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Jaddada Ƙudirin Ƙarfafa Ƙawance Da Indonesiya

by Sulaiman
2 years ago
Indonesiya

Gwamnatin Tarayya ta jaddada ƙudirin ta na zurfafa alaƙar ta da ƙasar Indonesiya, tare da mai da hankali kan batun tattalin arziki da kuma hanyoyin haɗin gwiwa.

 

An tabbatar da hakan ne a taron Indonesiya da nahiyar Afrika karo na biyu, wanda ake gudanarwa daga ranakun 1 zuwa 3 na Satumba, 2024, a Bali, babban birnin ƙasar.

ADVERTISEMENT
  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 
  • Zanga-zanga: Ana Tuhumar Mutane 10 Da Laifin Cin Amanar Kasa

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa Babban Taron Haɗin Gwiwa na Masu Ruwa da Tsaki da kuma Taron Shugabanni a ƙasar da ke nahiyar Asiya.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Ministan ya nanata ƙudirin Nijeriya na ƙulla ƙawance da Indonesiya, yana mai cewa dukkan yankunan biyu suna da abubuwa da yawa da za su samu daga ƙara haɗin gwiwa a fannin kasuwanci, zuba jari, da musayar ilmi da ƙwarewa.

 

Ya ce: “Taron Indonesiya da Afirka wata hanya ce ta haɗin gwiwa, da nufin ciyar da ƙasashen mu biyu zuwa makoma mai haske da wadata.”

 

Idris ya ƙara da cewa, “Nijeriya ta ƙudiri aniyar yin amfani da ƙarfin da muke da shi da albarkatun mu don mai da hankali kan muhimman ginshiƙai kamar sauyin tattalin arziki, makamashi da haƙar ma’adinai, samar da abinci da lafiya, da tattalin arziki na dijital.

 

“Waɗannan su ne ginshiƙan da za a gina haɗin gwiwar mu a nan gaba, tare da zurfafa haɗin gwiwa da cigaban tattalin arziki mai ɗorewa wanda zai amfani dukkan al’ummomin mu.”

 

Taron ya jaddada gagarumin ƙarfin tattalin arziki da al’ummar Afirka da Indonesiya suke da su, waɗanda ke wakiltar sama da mutane biliyan 1.7 da jimillar ƙarfin tattalin arziki na GDP na dalar Amurka tiriliyan 4.4.

 

Taron ya tattaro shugabannin ƙasashe, jami’an gwamnati, ‘yan kasuwa, da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban, inda suka tattauna haɗin gwiwar tattalin arziki, da magance matsalolin duniya, da kuma lalubo hanyoyin samun cigaba mai ɗorewa tare.

 

Jagorancin Nijeriya wajen ciyar da ajandar Tarayyar Afirka ta 2063 shi ma ya kasance jigon tattaunawa a taron.

 

Ministan ya yi bayani kan cikakkiyar ajandar Shugaban Ƙasa Tinubu ta sauye-sauyen tattalin arziki, tsaro, shugabanci, da cigaban al’umma a matakin ƙasa, da kuma ƙoƙarin da yake yi na inganta harkokin kasuwanci a yankin, da ababen more rayuwa, da kwanciyar hankali a siyasance ta hanyar jagorancin sa a Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS).

 

An bayyana rawar da Nijeriya ke takawa a Yankin Kasuwanci na Nahiyar Afirka (AfCFTA) a matsayin babbar hanyar bunƙasa kasuwanci da masana’antu a cikin Afirka.

 

Taron, wanda ya samu halartar wakilai daga ƙasashen Afirka 22 da kuma wasu ƙasashe biyar da ba na Afirka ba, ya kuma tuna da taron nahiyoyin Asiya da Afirka na shekarar 1955, wanda aka fi sani da “Bandung Spirit”, wanda ya aza harsashin dangantakar Asiya da Afirka.

 

Taron ya yi kira da a ƙara inganta yin mu’amala a tsakanin nahiyoyi ta fuskar kasuwanci, zuba jari, da haɗin gwiwar raya ƙasa.

 

An jaddada cewa kamata ya yi Afirka ta zarce matakin mai fitar da ɗanyen man fetur kawai, ta zama cibiyar samar da kayayyaki, tare da ba da tabbaci na musamman ga ayyukan bututun iskar gas da ke ratsa sahara tsakanin Nijeriya da Aljeriya da kuma Moroco.

 

Taron na Indonesiya da Afirka ya kasance wani dandali na ƙarfafa dangantakar tattalin arziki tsakanin Indonesiya da ƙasashen Afirka.

Indonesiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Zanta Da Shugaban Najeriya

Shugaba Xi Ya Zanta Da Shugaban Najeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.