An bude bikin baje kolin hada-hadar samar da kayayyaki na kasa da kasa na kasar Sin ko CISCE karo na hudu a ranar 22 ga watan nan a birnin Beijing. A wannan rana, an fitar da wata manufa mai taken “Inganta daidaito ta hanyar amfani da jarin kasashen waje” a hukumance.
“Goyon bayan da kasar Sin ke bai wa jarin kasashen waje ba ya tsaya a kan kalmomi ne kawai ba, ya kunshi ayyuka na zahiri,” kuma “Wannan manufar na kara mana kwarin gwiwa wajen zuba jari a kasar Sin”, irin wadannan kalmomi sun fito ne daga cikin ra’ayoyin shugabanni kusan 20 dake da kamfanoni na kasa da kasa da ma kungiyoyin kasuwanci na kasa da kasa, inda sun bayyana hakan ne yayin da suka zanta da wakilan CMG a wurin baje kolin.
A yayin da suke tsokaci kan fa’idojin tsarin masana’antu na kasar Sin kuwa, sun yaba wa yanayin kasuwancin kasar sosai.(Safiyah Ma)














