Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu kan kalaman da ke nuna cewa kafafen yaɗa labarai na ƙara bayyana matsalolin tsaro da tattalin arziƙi a Nijeriya fiye da yadda suke zahiri.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Atiku ya ce ‘yan Nijeriya ba sa buƙatar jaridu, talabijin ko ‘yan jarida su faɗs musu cewa suna cikin wahala.
Ya ce iyaye da ke fama wajen gaza ciyar da iyalansu da kuma jama’ar da ke fama da tashin farashin kayayyaki sun san halin da suke ciki ba tare da rahotannin kafafen yaɗa labarai ba.
Atiku ya ce ɗora wa kafafen yaɗa labarai laifin bayyana matsalolin ƙasar alama ce ta cewa gwamnati ba ta damu da halin da talakawa ke ciki ba.
Ya ce miliyoyin ‘yan Nijeriya na fama da tsadar rayuwa da rashin aikin yi.
Har ila yau, ya ce kafafen yaɗa labarai ba su ƙirƙiri labaran kashe-kashen da ake yi a jihohin Benue da Filato ba, ko hare-haren ‘yan bindiga a Zamfara, Katsina da Neja, ko kuma yawaitar garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma soki iƙirarin cewa yawancin sace-sacen mutane na faruwa ne saboda mutane suna tafiye-tafiye cikin dare.
Atiku ya jaddada cewa alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a na kan gwamnati ne, ba kan talakawa ba.
Ya kuma kare aikin ‘yan jarida, yana mai cewa aikinsu shi ne bayar da rahoton gaskiya da kuma isar da muryar jama’a.
A ƙarshe, Atiku ya buƙaci gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen magance matsalolin tattalin arziƙi da tsaro maimakon musanta abin da jama’a ke fuskanta.
“Nijeriya ba ta buƙatar bayyana irin wahala da ake ciki, tana buƙatar mafita,” in ji shi.














