Mataimakin shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, Hon. Abdussamad Dasuki, ya bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da ya gyara dangantaka da Jamhuriyar Nijar domin inganta tsaron iyakokin Arewa- maso- Yamma.
Dasuki wanda ke wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal a jihar Sakkwato ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da ya ziyarci hedikwatar jam’iyyar ADC ta jiha a inda ya jaddada muhimmancin kyautata hulda da makwabtan kasashe wajen magance matsalolin tsaro.
Dan majalisar ya bai wa gwamnoni shawara da su roki Shugaban Kasa da ya tabbatar an inganta dangantaka da makwabtan kasashe musamman Jamhuriyar Nijar.
A cewarsa halin da dangantaka tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar ke ciki a yanzu ba abin jin dadi ba ne kuma ba alama ce mai kyau ga kalubalen sha’anin tsaro da ke addabar kasar nan ba. Kyakkyawar hulda tsakanin kasashen biyu na da matukar muhimmanci wajen dakile matsalolin tsaro da ke addabar yankunan kan iyaka.
Dan majalisar ya kuma bukaci gwamnati ta dauki karin matakai domin magance matsalar tsaro, ciki har da daukar ma’aikatan tsaron dazuka da kuma karawa hukumomin tsaro kudade.
Dasuki ya jaddada cewa samar da wadannan matakai za su taimaka matuka wajen dakile ayyukan ‘yan ta’adda da kuma inganta tsaro a yankunan karkara.
Haka kuma ya bukaci gwamnonin jihohi a fadin kasar nan da su tanadi isassun kudade domin aiwatar da shirin kafa ‘yansandan jihohi, yana mai cewa hakan na da muhimmanci wajen kusantar da tsaro ga al’umma da kuma magance matsalolin tsaro cikin gaggawa.













