Majalisar Dattawan Nijeriya ta yi watsi da tsarin kaɗa ƙuri’a ta hanyar na’ura wajen duba kudirin kafa ‘Yansandan Jihohi da sauran kudirorin gyaran kundin tsarin mulki, inda ta amince da tsarin kiran sunayen sanatoci ɗaya bayan ɗaya domin su bayyana matsayinsu a fili.
An sanar da wannan mataki ne a zaman majalisar na ranar Laraba bayan wata bukata da shugaban masu rinjaye a majalisar, Opeyemi Bamidele, ya gabatar.
Bamidele ya bayyana cewa wasu na’urorin kaɗa ƙuri’a da sanatoci ke amfani da su, ba su aiki yadda ya kamata, lamarin da zai iya hana wasu daga cikin sanatocin damar kaɗa ƙuri’arsu.
Ya ce, “Maimakon mu yi amfani da tsarin zaɓe ta hanyar na’ura wanda a bayyane yake hakan zai iya hana wasu daga cikin takwarorinmu damar kaɗa ƙuri’a saboda matsalar na’urorinsu, ina neman a bai wa kowane Sanata damar bayyana matsayinsa ta hanyar amsa sunansa yayin kaɗa ƙuri’a.”
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya goyi bayan wannan shawara, yana mai cewa tsarin zaɓen a bainar jama’a zai ƙara tabbatar da gaskiya da riƙon amana.
A cewarsa, hakan zai bai wa al’ummar mazabun sanatocin damar sanin yadda wakilansu suka kada ƙuri’a kan muhimman batutuwan da suka shafi kundin tsarin mulkin ƙasa, musamman batun kafa rundunar ‘yansandan jihohi.














