Wani babban jami’in ma’aikatar shari’a ta kasar Sin ya ce tanadin da ke cikin dokar karfafa hadin kan kabilu da ciyar da su gaba, wadda ta ba da damar gurfanar da kungiyoyi da daidaikun mutane da ke wajen kasar masu hannu cikin ayyukan ballewar kabilu, ya dace bisa adalci a kan tsarin doka kuma ya kasance wajibi.
Jami’in wanda shi ne mataimakin ministan shari’a na kasar Sin, Hu Weilie, ya bayyana hakan ne a yau Laraba, yayin wani taron manema labarai da aka shirya domin gabatar da dokar, inda ya musanta zargin da wasu kafafen yada labarai na kasashen yamma suka yi cewa, sashe na 63 na dokar ya ba da damar “wuce gona da iri” ko “aiwatar da ita a wajen iyakokin kasar”.
Hu ya ce tanadin dokar ya yi daidai da ka’idojin shari’a, da yanayin dokokin kasa da kasa, da kuma abin da aka saba aiwatarwa a kasashe da dama.
An amince da dokar ne dai a zaman shekara-shekara na majalisar dokokin kasar Sin da aka gudanar a watan Maris na bana, kuma ana sa ran za ta fara aiki daga watan Yuli. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)













