Hakimin Makarfi, Alhaji Adamu Abdullahi, ya yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kan sake gina da zamanantar da Babban Asibitin Makarfi, yana mai cewa aikin ya kawo karshen shekaru da dama na sakaci tare da sauya yanayin kiwon lafiya a yankin.
Ya bayyana cewa tun bayan kafa asibitin a farkon shekarun 1970, ba a taba gudanar da wani gagarumin aikin gyara ko samar da kayan aikin zamani ba sai a ƙarƙashin gwamnatin Sanata Uba Sani.
Hakimin ya yi wannan jawabi ne yayin rangadin ayyukan ci gaba da gwamnatin jihar ke aiwatarwa a shiyya ta daya, ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu, Malam Ahmed Maiyaki, da Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma K. Ahmad.“Mutanenmu sun sha wahala tsawon shekaru saboda ƙarancin kayan aiki da ingantattun ayyukan lafiya. Yanzu kuma an kawo ƙarshen wannan matsala ta hanyar sake gina asibitin da samar masa da kayan aiki na zamani,” in ji Hakimin.
Ya kara da cewa aikin ya dawo da amincewar jama’a ga asibitocin gwamnati tare da samar wa dubban mutane damar samun kulawar lafiya mai inganci kusa da gidajensu.Wata mazauniyar yankin, Malama Sadiya Rabiu, ta ce sabon fasalin asibitin ya rage mata da sauran jama’a wahalar zuwa wasu garuruwa domin neman magani.“A yau muna samun kulawar lafiya mai kyau a gida. Wannan babban sauyi ne ga iyalai da dama,” in ji ta.
Shi ma Abdullahi Musa ya bayyana cewa aikin ya nuna yadda gwamnatin Uba Sani ke ba da fifiko ga walwalar talakawa da ci gaban al’umma.Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma K. Ahmad, ta ce asibitin Makarfi na daga cikin asibitoci 16 da ake sake ginawa da zamanantarwa a faɗin jihar domin ƙara inganta harkokin kiwon lafiya














