ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS), CGI Isah Jere Idris, ya amince da sauya wuraren aiki ga manyan jami’ai 69 zuwa manyan ofisoshin hukumar na shiyyoyi da jihohi da ke sassan ƙasar nan.

  • NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa daga cikin adadin jami’an da aka sauya wa wuraren aikin akwai masu muƙaman ƙananan Mataimakan Kwanturola Janar (ACG) guda takwas sai masu muƙaman Kwanturololi (CIS) guda 61 da aka rarraba su a sassan manyan ofisoshin hukumar.

Cikin masu muƙaman ACG da aka sauya wa wuraren aikin akwai ACG KM Amao wanda a da yake Kwanturolan Jihar Ogun amma yanzu an maida shi Sashen Ayyuka Na Gaba ɗaya a shalkwatar hukumar da ke Abuja, sa’ilin da ACG KN Nandap wanda a baya yake kula da Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas a yanzu kuma aka sauya masa zuwa Sashen Bayar da Takardu ga Baƙin Waje (CERPAC) a shalkwata.

ADVERTISEMENT

 

Har ila yau, ACG Abdullahi M Usman a yanzu shi ne Shugaban Sashen Kula da Shige da Fice na Yau da Kullum a shalkwatar hukumar, yayin da ACG BN Alawode ya zama Shugaban Sashen Kula da Walwala da Daidaiton Jinsi, sai kuma ACG EC Esedo da aka mayar zuwa Ofishin Shiyya ta huɗu da ke Minna.
Shi kuwa ACG MA Ushie na Sashen Yaƙi da Damfara an mayar da shi zuwa Sashen Difilomasiyya da Fasfo, sai ACG ES Fagbamigbe wanda a da yake kula da Babban ofishin Iyaka na Idi-Iroko da aka tura ya zama shugaban kula da iyakokin ƙasa na kan-tudu a shalkwata.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Daga cikin masu muƙaman Kwanturololi da aka sauya wa wuraren aikin kuwa akwai Compt. AO Adesokan da aka mayar zuwa Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas daga Sashen Horaswa da Inganta ƙwazon Ma’aikata, yayin da muƙaddashin babban jami’in ofoshin Kwanturola Janar, Compt. Ahmed Mustapha ya zama sabon Kwanturolan Kano. Sauran sun haɗa da Compt. Shittu Olajire Fatai wanda a yanzu aka mayar da shi Ofishin Kula da Iyaka na Legas; da Compt. Gwama Muhammad wanda a yanzu shi aka ba shugabancin Ofishin kula da iyaka na Idi-Iroko; da Compt. MM Saddiƙ wanda a yanzu aka ba shi matsayin Babban Jami’in Ofishin Kwanturola Janar.

Shi kuwa Compt. AO Bewaji an mayar da shi ne zuwa shalkwatar hukumar yayin da Compt. Michael Dike ya karɓi ragama a matsayin Kwanturolan Iyaka na Seme da ke Legas. Shi kuwa Kwanturola mai kula da ɗa’ar aiki an tura shi ya shugabanci yankin Jihar Osun yayin da Compt. Sabo A Rano da ya kasance Kwamandan Makarantar Horas da Jami’ai ta Kano aka mayar da shi zuwa Jihar Gombe.

Bugu da ƙari, Compt. FD Dakat na Sashen kula da tasoshin ruwa aka mayar da shi zuwa Jihar Akwa Ibom inda zai karɓi ragama daga Compt. GE Didel wanda aka mayar zuwa sashen shige da fice a shalkwata, da dai sauransu.

Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere ya hori dukkan jami’an da aka sauya wa wuraren aikin su yi amfani da basirar da Allah ya yi musu a wuraren da aka tura su wajen inganta aiki da tsaron ƙasa. Sauyin aikin dai ya fara aiki ne nan take.

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Jami’an Diflomasiyyar Afirka Na Fatan Kara Kulla Huldar Tattalin Arziki Da Kasar Sin

Jami’an Diflomasiyyar Afirka Na Fatan Kara Kulla Huldar Tattalin Arziki Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.