Tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, ya kai ziyarar girmamawa ga tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a daren Talata.
Jagororin jam’iyyar NDC biyun, sun gana ne jim kaɗan bayan kwamitin tantance ‘yan takara na jam’iyyar ya amince da Obi domin shiga zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba, Kwankwaso ya tabbatar da ganawar a gidansa da ke Maitama a Abuja.
Ya bayyana Obi a matsayin “ɗan uwana” tare da nuna kyakkyawan fata kan makomar jam’iyyar.
“Daren jiya, na karɓi ziyarar girmamawa daga ɗan uwana, Mai Girma Peter Obi, jim kaɗan bayan nasarar tantance shi a matsayin mai neman takarar shugaban ƙasa na jam’iyyarmu ta NDC. Gaba na cike da haske da alkawari,” in ji Kwankwaso.














Discussion about this post