Shugaban tawagar Sin, kuma shugaban hukumar kiwon lafiya ta kasar Lei Haichao a jiya Talata 19 ga watan, a cikin jawabinsa yayin muhawarar da aka yi a babban taron kiwon lafiya na duniya (WHA) karo na 79, ya bayyana cewa, gyare-gyaren tsarin kiwon lafiya na duniya dole ne ya ci gaba da zama a karkashin jagorancin kasashe mambobi, tare da baiwa kasashe masu tasowa damar fada a ji da kuma bukatunsu, kana da inganta daidaiton ci gaban lafiya a duniya.
Lei Haichao ya kara da cewa, cikin shekaru 60 da suka gabata, kasar Sin ta tura ma’aikatan lafiya 31,000 na agaji zuwa kasashen waje, tare da kula da jinyar marasa lafiya miliyan 300, kuma ta kirkiro maganin zazzabin cizon sauro na Artemisinin, inda ta bayar da “gudunmawa irin ta Sin” don inganta samun daidaito a bangaren kiwon lafiya a duniya. Bugu da kari, Sin tana matukar goyon bayan tsarin hadin gwiwar bangarori da yawa, kuma tana goyon bayan matsayin kungiyar lafiya ta duniya (WHO) da rawar da take takawa wajen daidaita ayyukan kiwon lafiya na duniya, tare da hadin gwiwa da bangarori daban-daban, don inganta tsarin kiwon lafiya na duniya ya zama mafi adalci, daidaito da kuma inganci. Ban da wannan kuma, wakilin Sin na dindindin a ofishin MDD dake birnin Geneva na Switzerland da sauran kungiyoyin kasa da kasa, Jia Guide ya yi jawabi a madadin “rukunin abokan inganta tsarin shugabancin duniya” ta Geneva, inda ya yi kira da a gina ingantaccen tsarin kiwon lafiya na duniya mai adalci, da inganci da kuma hadewa da juna.
Jia Guide ya nuna cewa, a halin yanzu tsarin kiwon lafiya na duniya yana fuskantar kalubale da dama. Inganta tsarin kiwon lafiya na duniya nauyi ne dake rataya a wuyar kowa da kowa don kare lafiyar jama’a da inganta ci gaba mai dorewa.
Ya kamata bangarori daban-daban su rike manyan ka’idoji uku, na farko, nacewa ga shiga ayyukan tsari cikin daidaito, ta yadda za a saurari ra’ayoyi da damuwar bangarori daban-daban, musamman na kasashe masu tasowa. Na biyu, tsayin tsaya daka kan hadin gwiwar bangarori da yawa. Na uku, kiyayewa da kuma mutunta muradun bil’adama, da kula da ainihin bukatun al’ummun kasashe masu tasowa.
A watan Fabrairun bana ne aka kaddamar da “rukunin abokan inganta tsarin shugabancin duniya” ta Geneva bisa kokarin bangaren Sin, wadda ta zama wani dandali mai kyau ga bangarori daban-daban su rika tattaunawa kan sake fasalin tsarin shugabancin duniya da inganta shi. Ya zuwa yanzu, rukunin yana da kasashe mambobi 47. (Amina Xu)















Discussion about this post