Kasar Sin ta fitar da wani shiri mai wa’adin shekaru 5 ga tsarinta na kasa na tallata kayayyaki da samar da su, da nufin karfafa hidimomin aikin gona da tabbatar da wadatar abinci tsakanin shekarar 2026 zuwa 2030.
Gamayyar kungiyoyin tallata kayayyaki da samar da su ta kasar Sin, ta ce shirin ya zayyana wasu manyan ayyuka 18, wadanda ke mayar da hankali kan tabbatar da wadatar abinci da inganta farfado da yankunan karkara.
Zuwa shekarar 2030, tsarin zai gina ko gyara muhimman cibiyoyin adana taki na matakin kasa sama da guda 100, da kuma kimanin cibiyoyi 1,000 na rarraba kayayyaki na matakin gunduma, a manyan gundunmomi masu samar da hatsi.
Kungiyoyin tallata kayayyaki da samar da su, kungiyoyi ne da ke tallafawa aikin gona da yankunan karkara da manoma, karkashin shugabancin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin. Kuma suna zaman muhimmiyar hanyar da jam’iyyar da gwamnati ke bi wajen aiwatar da ayyukan da suka shafi aikin gona da yankunan karkara da manoma, kuma wani babban karfi ne na inganta raya yankunan karkara da aikin gona na kasar Sin.
Bisa wani tsari da ya shafi fadin kasar, shirin zai kasance wata muhimmiyar mahada tsakanin kasuwannin birane da na kauyuka. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














