Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta yi gargadin cewa maniyyatan da suka gaza miƙa ingantattun fasfofinsu na tafiya kafin ranar 25 ga Agusta na iya rasa damar samun kujerun aikin Hajjin 2026.
Babban Daraktan hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim-Matawalle, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sulaiman Dederi, ya sanya wa hannu a ranar Asabar a Kano.
Hukumar ta ce sanya wa’adin ya zama dole ne domin ba ta damar kammala rajista da shirye-shiryen takardun maniyyatan da suka yi rajista kafin fara aikin Hajjin.
Hukumar ta buƙaci dukkan maniyyatan da suka yi rajista waɗanda ba su miƙa fasfofinsu ba da su tabbatar sun miƙa su kafin ko a ranar 25 ga Agusta.
Ta kuma yi gargadin cewa ba za ta ɗauki alhakin duk wata matsala ko sakamakon da zai biyo bayan rashin bin wannan wa’adi ba.
Saboda haka, hukumar ta shawarci dukkan maniyyatan da abin ya shafa da su ɗauki umarnin da muhimmanci tare da gaggauta miƙa fasfofinsu cikin wa’adin da aka kayyade.














