Bisa labarin da kwamitin kiwon lafiya na kasar Sin ya fitar, da safiyar yau Jumma’a, rukuni na biyu na tawagar kwararrun likitoci ta Sin, ya tashi daga birnin Beijing zuwa jamhuriyyar demokradiyar Kongo don karbar ragamar aiki daga rukunin tawagar ta farko, tare da yin hadin gwiwa da kasashen duniya don gudanar da ayyukan kandagarki da shawo kan cutar Ebola, ta yadda za a ci gaba da taimaka wa yankin wajen kare lafiyar jama’a.
A cewar wani jami’in kwamitin kiwon lafiya na kasar Sin, bayan rukuni na biyu na tawagar kwararrun likitocin ya isa jamhuriyar demokradiyyar Kongo, zai karbi ragamar aiki daga tawagar ta farko, kuma zai yi aiki tare da tawagar likitoci ta Sin dake aiki a kasar, don karfafa tantance yaduwar cutar ta Ebola, da musayar darussan rigakafin annobar da hukumomin kula da cututtuka da abin ya shafa, da inganta hadin gwiwa, da kafa tsarin hadin gwiwa na yau da kullun da kungiyoyin kasa da kasa, da shiga cikin ayyukan yaki da annobar na kasa da kasa, da kuma taimakawa yankin wajen inganta karfin kandagarki da shawo kan cutar ta Ebola. (Safiyah Ma)














