Shugaban ƙaramar hukumr Gwale, Hon Abubakar Muazu Mojo ya bayyana cewa sakamakon ƙoƙarin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf na ganin an sama wa matasa aikin yi da kuma bunƙasa ilimi a Jihar Kano, yanzu haka matasa maza da mata 521 sun karɓi takardun zama cikakkun ma’aikatan gwamnati a Gwale.
Ya ce matasan waɗanda aka ɗauka aikin koyar a makarantu daban-daban kamar yadda gwamna ya amince a ƙaramar hukumar Gwale.
Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana haka ne a taron miƙa takardun amincewa ga waɗannan matasa wanada aka gabatar a ƙaramar hukumar Gwale a Jihar Kano.
Haka kuma Hon Mojo ya ƙara da cewa gwamnan Kano mai kishin ilimi ne da zaman lafiya da duk wani abu da zai kawo wa al’ummar Kano ci gaba, wanda wannan ce ta sa ake ta ayyuka na ci gaba a kowanne fanni.
Shi ma a jawabinsa, sakataren ilimi na ƙaramar hukumar Gwale kuma shugaban ƙungiyar sakatarorin ilimi, Es Mukhatri Inuwa ya ce wannan babban ci gaba ne a fannin ilimi, domin ilimi shi ne gishirin zaman duniya.
Ya kuma buƙaci malaman da aka ɗauka da su saka kishin ilimi da tarbiyya don yin aiki tuƙuru yadda kwalliya za ta biya kuɗin sabulu.
Mai Magana da yawun kansilolin ƙaramar hukumar Gwale, Hon Nura Adamu da shugabar mata ta ƙaramar hukumar Gwale, Hajiya Ruƙayya na daga cikin waɗanda suka yi jawabin nuna gamsuwa da wannan ƙoƙari na ɗaukar malamai 521.














