Rundunar ‘yantar da al’ummar Sinawa ta PLA, ta ce ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen murkushe masu rudin kansu da neman ‘yancin kan Taiwan, kuma za ta tabbatar da kare cikakken ‘yanci da yankunan kasar Sin.
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Zhang Xiaogang ne ya bayyana haka a yau Alhamis yayin wani taron manema labarai, lokacin da ya ke amsa tambaya game da batun.
A cewarsa, yankin Taiwan mallakin kasar Sin ne, kuma babu mai daukakawa da ganin darajar zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin Taiwan fiye da kasar Sin.
Sai dai kuma, ba za su taba barin wani mutum ko wani karfi ya raba Taiwan da kasar Sin ta kowace hanya ba. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post