ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sai Da Ruwan Ciki Ake Jan Na Rijiya

by CGTN Hausa
3 years ago
Rijiya

Sanin kowa ne cewa, babbar matsalar dake addabar wasu sassan duniya a halin yanzu shi ne, batun abinci ko cimaka, sakamakon fadace-fadace, da matsalar fari, ambaliyar ruwa da ta yi awon gaba da amfanin gona ko wasu matsaloli masu nasaba da matsalar sauyin yanayi ko kuma bala’u daga indallahi. Wannan ne ma ya sa, a duk lokacin da aka shirya taruka a lokuta mabambanta ake kira ga kasashen duniya su ba da muhimmanci ga batun samar da abinci, da ma ingantacciyar hanyar warware matsalar ta hanyar hadin gwiwa.

Masana sun sha bayyana cewa, tsarin samar da abinci na duniya “ya tabarbare”, kuma wajibi ne a canza hanyar samar da abinci, da kuma yadda ake amfani da shi, a halin yanzu ta yadda zai dace da ci gaban zamani.

  • An Yabawa Sin Kan Taimakon Ilimi Ga Dalibai Masu Rauni A Habasha 
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Intanet Na Tauraron Dan Adam

Ko da a shawarar da ya gabatar game da raya kasa da kasa, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya sanya batun samar da abinci a matsayin daya daga cikin muhimman fannoni guda takwas na hadin gwiwa. Kuma kasar Sin ta gudanar da hadin gwiwa a fannin aikin gona tare da kasashe da yankuna fiye da 140, da inganta fasahohin aikin gona sama da dubu guda ga kasashe masu tasowa, lamarin da ya haifar da karuwar yawan amfanin gona da sama da kashi 30 zuwa 60 cikin 100 a yankunan da suka ci gajiyar wannan tsari.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kasar Sin ta horar da dubban kwararru masu sana’ar noman irin shinkafa da aka tagwaita ga kasashe masu tasowa sama da 80, ta kuma gina yankunan gwaji na bunkasa aikin gona, da rage talauci masu tarin yawa, wanda hakan ya taimakawa kasashe masu tasowa, wajen kara kwarewar inganta ayyukan noma da samar da abinci.

Bayanai na nuna cewa, duk da wadannan matakai akwai tarin jama’a a sassan duniya dake fama da yunwa sakamakon wasu matsaloli ko dalilai ko matakan kashin kai da wasu kasashen yamma suka dauka. Matakai da tsare-tsare da kasar Sin ke bijiro da su karkashin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, sun taimaka matuka wajen kara samar da abinci da ma dabarun noma iri-iri a sassan nahiyar.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Masana na cewa, kasashen Afrika za su iya amfani da huldar dake tsakanin Sin da nahiyar, wajen kawo gagarumin sauyi a tsarin aikin gona, da magance yunwa, da karancin sinadarai masu gina jiki, da kuma habaka tattalin arzikin mazauna yankunan karkara. Uwa uba da matakan magance matsalar sauyin yanayi masu saukin aiwatarwa, wadda shi ne ke haifar da matsalar karancin cimaka.

A yayin da sassa masu ruwa da tsaki a babban taron sauyin yanayi na COP28 a birnin Dubai na hadaddyar daular Larabawa ke fatan tara dalar Amurka biliyan 270 don samar da kudaden tunkarar tasirin yanayi nan da shekarar 2030, wajibi ne shugabanni su dauki matakai tare da cika alkawuran da suka dauka a yayin taron da ma tarukan da suka gabata, don takaita karuwar yanayin zafin duniya zuwa ma’aunin digirin Celcius 1.5, don kare duniyarmu baki daya daga tasirin sauyin yanayi, ta yadda za a kai ga gina duniya mai tsafta da kowa ne bil-Adama zai ji dadin zama a cikinta.

Wannan na kara nuna cewa, idan har ana son wadata kasa da abinci, ya kamata mahukunta su taimakawa manoma da muhimman kayayyakin noma na zamani da ake bukata, ta yadda za su samar da abincin da al’umma ke bukata da ma samun karin kudin shiga, da raya kauyuka, da kuma ci gaba da zamanintar da aikin gona. Sanin kowa ne cewa, abinci shi ne tushen rayuwa. Kamar yadda malam Bahaushe ke cewa, sai da ruwan ciki ake jan na rijiya. Kuma sai ciki ya koshi kafin a iya yin komai na rayuwa.

Rijiya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Ta Dauki Alhakinta Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.