ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Shehu Sani Ya Buƙaci Al’ummar Kaduna Su Zaɓi Mutane Masu Mutunci A Zaɓen 2027

by Sulaiman
9 months ago

Daga Shehu Yahaya Kaduna.

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bukaci al’ummar Jihar Kaduna da su yi tunani mai zurfi tare da natsuwa wajen zaɓar shugabanni nagari a zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

 

ADVERTISEMENT

Sanata Shehu Sani ya ce lokaci ya yi da al’ummar jihar Kaduna za su bai wa gwamnatin Gwamna Uba Sani cikakken goyon baya, bisa la’akari da ayyukan ci gaban da gwamnatinsa ke aiwatarwa a fadin jihar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 5 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kano.
  • Sin Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Bunkasa Tsimin Makamashi Da Rage Fitar Da Hayakin Carbon

Ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi bakwancin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC daga Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, a gidansa da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

 

A cewarsa, al’ummar Kaduna ya kamata su yi hattara da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufa’i, musamman dangane da duk wani yunkuri da yake yi na tallata dan takara ta jam’iyyar ADC.

 

Sanata Shehu Sani ya tunatar da jama’a abubuwan da suka faru a tsakanin shekarun 2015 zuwa 2023, inda aka rushe gidaje tare da korar mutane da dama daga aikinsu. Ya ce a halin yanzu Allah ya albarkaci jihar Kaduna da gwamna mai tausayi, dattako da mutunta jama’a, wanda baya amfani da kafafen yada labarai wajen zagin mutane.

 

“Ba za mu koma gidan jiya ba,” in ji Sanatan. “Mutumin da ya yi barna shi ne yanzu yake yawo yana neman goyon bayan jama’a. Ku yi hattara kada ku bari a sake maimaita abin da ya faru.”

 

Ya kara da cewa Gwamna Uba Sani ya ware Naira miliyan 100 ga kowacce mazaba domin ayyukan ci gaba, tare da bukatar jama’a su tabbatar sun amfana da irin wadannan tsare-tsare na alheri.

 

Sanata Shehu Sani ya ce akwai yunkurin dawowar tsohon gwamna domin tsayar da wani gwamna a jihar Kaduna, inda ya gargadi al’umma da kada su bari hakan ya faru, domin kada a koma rushe gidaje da korar jama’a bisa wasu hujjoji.

 

A karshe, ya jaddada cewa Gwamna Uba Sani ya mutunta al’ummar Kaduna, don haka ya dace jama’a su biya wannan alheri ta hanyar hada kai da zabar mutane masu mutunci da nagarta, musamman ta hanyar goyon bayan jam’iyyar APC a zaben da ke tafe.

 

Ya ce zaben 2027 zai kasance zabe ne na makoma, inda al’ummar Kaduna za su zabi tsakanin ci gaba da komawa baya

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Next Post
Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.