ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Shehu Sani Ya Buƙaci Al’ummar Kaduna Su Zaɓi Mutane Masu Mutunci A Zaɓen 2027

by Sulaiman
6 months ago

Daga Shehu Yahaya Kaduna.

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bukaci al’ummar Jihar Kaduna da su yi tunani mai zurfi tare da natsuwa wajen zaɓar shugabanni nagari a zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

 

ADVERTISEMENT

Sanata Shehu Sani ya ce lokaci ya yi da al’ummar jihar Kaduna za su bai wa gwamnatin Gwamna Uba Sani cikakken goyon baya, bisa la’akari da ayyukan ci gaban da gwamnatinsa ke aiwatarwa a fadin jihar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 5 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kano.
  • Sin Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Bunkasa Tsimin Makamashi Da Rage Fitar Da Hayakin Carbon

Ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi bakwancin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC daga Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, a gidansa da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

 

A cewarsa, al’ummar Kaduna ya kamata su yi hattara da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufa’i, musamman dangane da duk wani yunkuri da yake yi na tallata dan takara ta jam’iyyar ADC.

 

Sanata Shehu Sani ya tunatar da jama’a abubuwan da suka faru a tsakanin shekarun 2015 zuwa 2023, inda aka rushe gidaje tare da korar mutane da dama daga aikinsu. Ya ce a halin yanzu Allah ya albarkaci jihar Kaduna da gwamna mai tausayi, dattako da mutunta jama’a, wanda baya amfani da kafafen yada labarai wajen zagin mutane.

 

“Ba za mu koma gidan jiya ba,” in ji Sanatan. “Mutumin da ya yi barna shi ne yanzu yake yawo yana neman goyon bayan jama’a. Ku yi hattara kada ku bari a sake maimaita abin da ya faru.”

 

Ya kara da cewa Gwamna Uba Sani ya ware Naira miliyan 100 ga kowacce mazaba domin ayyukan ci gaba, tare da bukatar jama’a su tabbatar sun amfana da irin wadannan tsare-tsare na alheri.

 

Sanata Shehu Sani ya ce akwai yunkurin dawowar tsohon gwamna domin tsayar da wani gwamna a jihar Kaduna, inda ya gargadi al’umma da kada su bari hakan ya faru, domin kada a koma rushe gidaje da korar jama’a bisa wasu hujjoji.

 

A karshe, ya jaddada cewa Gwamna Uba Sani ya mutunta al’ummar Kaduna, don haka ya dace jama’a su biya wannan alheri ta hanyar hada kai da zabar mutane masu mutunci da nagarta, musamman ta hanyar goyon bayan jam’iyyar APC a zaben da ke tafe.

 

Ya ce zaben 2027 zai kasance zabe ne na makoma, inda al’ummar Kaduna za su zabi tsakanin ci gaba da komawa baya

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.