ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Shehu Sani Ya Buƙaci Al’ummar Kaduna Su Zaɓi Mutane Masu Mutunci A Zaɓen 2027

by Sulaiman
7 months ago

Daga Shehu Yahaya Kaduna.

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bukaci al’ummar Jihar Kaduna da su yi tunani mai zurfi tare da natsuwa wajen zaɓar shugabanni nagari a zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

 

ADVERTISEMENT

Sanata Shehu Sani ya ce lokaci ya yi da al’ummar jihar Kaduna za su bai wa gwamnatin Gwamna Uba Sani cikakken goyon baya, bisa la’akari da ayyukan ci gaban da gwamnatinsa ke aiwatarwa a fadin jihar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 5 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kano.
  • Sin Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Bunkasa Tsimin Makamashi Da Rage Fitar Da Hayakin Carbon

Ya bayyana hakan ne yayin da ya karbi bakwancin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC daga Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, a gidansa da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

 

A cewarsa, al’ummar Kaduna ya kamata su yi hattara da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufa’i, musamman dangane da duk wani yunkuri da yake yi na tallata dan takara ta jam’iyyar ADC.

 

Sanata Shehu Sani ya tunatar da jama’a abubuwan da suka faru a tsakanin shekarun 2015 zuwa 2023, inda aka rushe gidaje tare da korar mutane da dama daga aikinsu. Ya ce a halin yanzu Allah ya albarkaci jihar Kaduna da gwamna mai tausayi, dattako da mutunta jama’a, wanda baya amfani da kafafen yada labarai wajen zagin mutane.

 

“Ba za mu koma gidan jiya ba,” in ji Sanatan. “Mutumin da ya yi barna shi ne yanzu yake yawo yana neman goyon bayan jama’a. Ku yi hattara kada ku bari a sake maimaita abin da ya faru.”

 

Ya kara da cewa Gwamna Uba Sani ya ware Naira miliyan 100 ga kowacce mazaba domin ayyukan ci gaba, tare da bukatar jama’a su tabbatar sun amfana da irin wadannan tsare-tsare na alheri.

 

Sanata Shehu Sani ya ce akwai yunkurin dawowar tsohon gwamna domin tsayar da wani gwamna a jihar Kaduna, inda ya gargadi al’umma da kada su bari hakan ya faru, domin kada a koma rushe gidaje da korar jama’a bisa wasu hujjoji.

 

A karshe, ya jaddada cewa Gwamna Uba Sani ya mutunta al’ummar Kaduna, don haka ya dace jama’a su biya wannan alheri ta hanyar hada kai da zabar mutane masu mutunci da nagarta, musamman ta hanyar goyon bayan jam’iyyar APC a zaben da ke tafe.

 

Ya ce zaben 2027 zai kasance zabe ne na makoma, inda al’ummar Kaduna za su zabi tsakanin ci gaba da komawa baya

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

Mamallaka Sana’o’i Masu Zaman Kansu “Bangare Ne Na Iyalinmu”

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.