Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya nuna damuwa kan yadda Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da karɓar bashi duk da cire tallafin man fetur.
Da yake magana a wata hira da da gidan talabijin na ‘News Central TV’ a ranar Juma’a, tsohon gwamnan na Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi gargadin cewa rashin tsauraran matakan kula da kuɗaɗen gwamnati na iya lalata ribar da ake sa ran samu daga sauye-sauyen tattalin arzikin da aka yi kwanan nan.
Sanusi, wanda ya daɗe yana sukar tsarin tallafin mai, ya sake jaddada cewa tsarin ba mai ɗorewa ba ne, yana mai sukar yadda ƙasar ta dogara da matatun mai na ƙasashen waje alhali matatun cikin gida ba sa aiki yadda ya kamata a baya.
“Bai da ce mu ci gaba da tallafa wa matatun mai na ƙasashen waje ba a matsayinmu na ƙasar da ke samar da mai, alhali matatunmu ba sa aiki,” in ji shi.
Sai dai ya amince cewa, an samu wasu ci gaba a ɓangaren, yana mai cewa Nijeriya ta fara daina dogaro sosai kan shigo da man fetur daga waje, inda yazo take iya tace mai sannan ta fitar da shi zuwa ƙasashen waje.
“Yanzu muna da matatar mai ta cikin gida. Ba ma shigo da kayayyakin man fetur kamar da; har ma muna fitar da su zuwa Turai. Wannan abu ne mai kyau ga tattalin arziki,” In ji shi















Discussion about this post