Magoya bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu sun yi watsi da sukar da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kan tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC na Musulmi da Musulmi.
Sun ce batun ba shi da wani tasiri a siyasa kuma ba zai zama abin tattaunawa ba yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.
Magoya bayan sun mayar da martani ne bayan Kwankwaso ya ce tikitin takarar Musulmi da Musulmi zai ci gaba da zama babban batu a zaɓen 2027, musamman ganin cewa Shugaba Tinubu ya ci gaba da tafiya da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa.
Da yake magana da manema labarai a Abuja a wani taron kwana ɗaya da ƙungiyar North Central Agenda (NCA) ta shirya kan ci gaban tattalin arziƙi, tsari da ayyukan more rayuwa a yankin Arewa ta Tsakiya ƙarƙashin gwamnatin Tinubu, Darakta Janar na Tinubu Support Group (TSG), Dakta Umar Tanko Yakasai, ya ce sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023 ya riga ya kawo ƙarshen wannan muhawara.
Yakasai ya ce mutane da dama sun yi hasashen cewa tikitin Musulmi da Musulmi zai hana Tinubu samun nasara a zaɓen 2023, amma duk da haka ‘yan Nijeriya sun zaɓe shi.
Ya ƙara da cewa yankin Arewa ta Tsakiya, duk da yawan Kiristocin da yake da shi, ya amfana da muƙaman gwamnati da kuma ayyukan more rayuwa a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.
A cewarsa, ya kamata a riƙa auna gwamnati bisa irin ayyukan da take yi, ba bisa addinin shugabanninta ba.
Ya kuma buƙaci ‘yan siyasa su mayar da hankali kan matsalolin da suka shafi ci gaban ƙasa maimakon sake tayar da muhawara kan addinin ‘yan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC.
Sai dai Kwankwaso ya bayyana cewa tikitin Musulmi da Musulmi zai ci gaba da kasancewa muhimmin batu a zaɓen 2027.
Ya ce ya yi mamakin yadda Shugaba Tinubu ya ci gaba da tafiya da wannan tsari duk da cece-kucen da ya haifar kafin zaɓen shekarar 2023.














