ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

by Sadiq
1 day ago

Magoya bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu sun yi watsi da sukar da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kan tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC na Musulmi da Musulmi.

Sun ce batun ba shi da wani tasiri a siyasa kuma ba zai zama abin tattaunawa ba yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Magoya bayan sun mayar da martani ne bayan Kwankwaso ya ce tikitin takarar Musulmi da Musulmi zai ci gaba da zama babban batu a zaɓen 2027, musamman ganin cewa Shugaba Tinubu ya ci gaba da tafiya da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa.

ADVERTISEMENT

Da yake magana da manema labarai a Abuja a wani taron kwana ɗaya da ƙungiyar North Central Agenda (NCA) ta shirya kan ci gaban tattalin arziƙi, tsari da ayyukan more rayuwa a yankin Arewa ta Tsakiya ƙarƙashin gwamnatin Tinubu, Darakta Janar na Tinubu Support Group (TSG), Dakta Umar Tanko Yakasai, ya ce sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023 ya riga ya kawo ƙarshen wannan muhawara.

Yakasai ya ce mutane da dama sun yi hasashen cewa tikitin Musulmi da Musulmi zai hana Tinubu samun nasara a zaɓen 2023, amma duk da haka ‘yan Nijeriya sun zaɓe shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

Ya ƙara da cewa yankin Arewa ta Tsakiya, duk da yawan Kiristocin da yake da shi, ya amfana da muƙaman gwamnati da kuma ayyukan more rayuwa a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.

A cewarsa, ya kamata a riƙa auna gwamnati bisa irin ayyukan da take yi, ba bisa addinin shugabanninta ba.

Ya kuma buƙaci ‘yan siyasa su mayar da hankali kan matsalolin da suka shafi ci gaban ƙasa maimakon sake tayar da muhawara kan addinin ‘yan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC.

Sai dai Kwankwaso ya bayyana cewa tikitin Musulmi da Musulmi zai ci gaba da kasancewa muhimmin batu a zaɓen 2027.

Ya ce ya yi mamakin yadda Shugaba Tinubu ya ci gaba da tafiya da wannan tsari duk da cece-kucen da ya haifar kafin zaɓen shekarar 2023.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Next Post
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.