Jam’iyyar NNPP ta yaba wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) bayan ta mayar da tambarin jam’iyyar na asali.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta maka INEC a kotu tare da neman diyyar Naira biliyan 10, tana zargin hukumar da jinkirta aiwatar da umarnin kotu.
Rikicin ya fara ne bayan wani ɓangare na jam’iyyar da ake dangantawa da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Buba Galadima ya yi ƙoƙarin karɓe ragamar jam’iyyar, lamarin da ya haifar da saɓani kan tambarin NNPP.
Daga bisani, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci INEC ta dawo da tambarin NNPP na asali tare da amincewa da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar.
Da yake magana da manema labarai a Abuja, Shugaban NNPP na ƙasa, Dakta Agbo Major, ya tabbatar da cewa INEC ta dawo da tambarin jam’iyyar mai “Kwandon ‘Ya’yan Itatuwa A Kan Taswirar Nijeriya.”
Ya ce hakan ya tabbatar da cewa shi da wanda ya kafa jam’iyyar, Dakta Boniface Aniebonam, su ne halastattun shugabannin NNPP.
Major ya kuma ce jam’iyyar ta fara shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen shekarar 2027 ta hanyar miƙa sunayen ‘yan takarar Majalisar Dokoki ta Ƙasa da kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na wucin gadi a shafin INEC.
Ya zargi INEC da rashin bin umarnin kotu saboda ba ta amince da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa na jam’iyyar cikin wa’adin da kotu ta bayar ba.
A cewarsa, wannan jinkiri ya jawo wa jam’iyyar asara, saboda haka lauyoyinta sun fara shirin shigar da ƙara tare da neman diyyar Naira biliyan 10 a wajen INEC.
Major ya kuma yi kira ga matasa, mata da ‘yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje da su shiga jam’iyyar NNPP.














