Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun ceto wasu mutane da aka yi garkuwa da su, sannan suka daƙile yunkurin sace mutane tare da kama wasu da ake zargi da kai wa ‘yan ta’adda kayan da suka kai wasu hare-hare a jihohin Zamfara, Katsina da Kebbi.
Rundunar sojin ta ce an gudanar da waɗannan ayyuka ne a ranakun 19 da 20 ga watan Yuli a ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a yankin Arewa maso Yamma.
A Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda ta Jihar Zamfara, sojoji sun kai ɗauki bayan samun kiran gaggawa cewa wasu ‘yan ta’adda na ƙoƙarin yin garkuwa da mutane a wani gida.
Da isar sojojin, maharan suka tsere, lamarin da ya sa aka kuɓutar da mutanen da ake shirin sacewa.
A Ƙaramar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina, sojoji sun ceto mutum uku da suka tsere daga hannun masu garkuwa da su yayin da ake ruwan sama mai ƙarfi, kuma maharan na barci.
An sace mutanen ne a ranar 14 ga watan Yuli yayin da suke aiki a gonakinsu da ke Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.
Daga bisani an miƙa su ga hukumomin da suka dace.
A Jihar Kebbi, sojoji sun tare wata mota ɗauke da babura 10 da ake zargin ana shirin kai wa ‘yan ta’adda ne.
Haka kuma, an kama mutane huɗu da ake zargi da hannu a lamarin, yayin da aka ƙwato baburan domin ci gaba da bincike.
Rundunar sojin ta yaba wa dakarun kan saurin ɗaukar mataki da kuma ƙwarewar da suka nuna wajen daƙile ayyukan ‘yan ta’adda.
Ta kuma gode wa al’umma kan ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai, tare da buƙatar su ci gaba da haɗa kai da hukumomin tsaro domin yaƙi da ta’addanci da sauran laifuka.













