ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Ceto Zamfara Na Samun Nasara, Yayin Da Gwamna Lawal Ke Duba Ayyuka A Shinkafi

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa shirin ceto jihar sa daga halin da take ciki, wato “Rescue Mission” yana tafiya yadda ya dace kuma yana haifar da gagarumin sakamako.

 

A ranar Laraba, gwamnan ya kai ziyarar aiki a Ƙaramar Hukumar Shinkafi domin duba manyan ayyukan da gwamnatin jihar sa ke aiwatarwa a yankin.

ADVERTISEMENT
  • NCoS Ta Kama Mutane 2 Bisa Yunƙurin Safarar Miyagun Ƙwayoyi Zuwa Gidan Yarin Kano
  • Ministan Wajen Sin Zai Ziyarci Kasashen Afirka Hudu Tare Da Halartar Wani Biki A Hedkwatar AU

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a lokacin ziyarar, Gwamna Lawal ya halarci bikin ƙaddamar da shirin tallafawa al’umma da ɗan majalisa mai wakiltar Shinkafi/Zurmi a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Bello Hassan Shinkafi, ya shirya.

 

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Shirin tallafin ya amfanar da mutane 2,000 ta hanyar raba motoci masu kyau, kekunan hawa, babura, injinan ɗinki da sauran kayan taimako.

 

A cikin wannan ziyara, Gwamna Lawal ya duba Cibiyar Kula da Mata da Yara (WCWC) a garin Shinkafi, wadda aka bayar domin cikakken gyara. Haka kuma, ya ziyarci Babban Asibitin na Shinkafi wanda aka gyara tare da sabunta kayan aikin sa, da kuma sabon asibitin gaggawa ‘Referral Hospital’ da ke nan a cikin garin.

 

A fadar Sarkin Shinkafi, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na aiwatar da manyan ayyuka a dukkan ƙananan hukumomin jihar.

 

Ya ce, “Mun zo Shinkafi yau domin duba muhimman ayyukan da gwamnatin mu ke gudanarwa tare da ƙaddamar da shirin tallafin ɗan majalisar tarayya, Hon. Bello Hassan Shinkafi.

 

“Mun kammala gyaran babban asibitin Shinkafi tare da samar masa da na’urori na zamani da za su taimaka wajen kula da lafiya cikin gaggawa ga al’umma.

 

“Sabon asibitin gaggawa zai zama jigo wajen inganta kiwon lafiya, ba kawai a Shinkafi ba, har ma ga dukan yankin arewacin Zamfara. Wannan zai rage wa jama’a wahalar neman kulawar likitoci.”

 

Gwamnan ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta mallaki tsohuwar makarantar Bafarawa domin mayar da ita Cibiyar Karatun Kimiyyar Lafiya ta Jami’ar Jihar Zamfara, inda ake ci gaba da aikin gyara don fara amfani da ita nan ba da jimawa ba.

 

Gwamna Lawal ya yaba wa Hon. Bello Hassan bisa irin wannan shirin taimakon al’umma, tare da kira ga sauran shugabanni da su mayar da hankali kan ci gaban ɗan adam.

 

SULAIMAN BALA IDRIS

Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara

7 ga Janairu, 2026

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
2027: Datti Baba-Ahmed Ya Ayana Neman Takarar Shugaban Ƙasa

2027: Datti Baba-Ahmed Ya Ayana Neman Takarar Shugaban Ƙasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.