ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Ceto Zamfara Na Samun Nasara, Yayin Da Gwamna Lawal Ke Duba Ayyuka A Shinkafi

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa shirin ceto jihar sa daga halin da take ciki, wato “Rescue Mission” yana tafiya yadda ya dace kuma yana haifar da gagarumin sakamako.

 

A ranar Laraba, gwamnan ya kai ziyarar aiki a Ƙaramar Hukumar Shinkafi domin duba manyan ayyukan da gwamnatin jihar sa ke aiwatarwa a yankin.

ADVERTISEMENT
  • NCoS Ta Kama Mutane 2 Bisa Yunƙurin Safarar Miyagun Ƙwayoyi Zuwa Gidan Yarin Kano
  • Ministan Wajen Sin Zai Ziyarci Kasashen Afirka Hudu Tare Da Halartar Wani Biki A Hedkwatar AU

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a lokacin ziyarar, Gwamna Lawal ya halarci bikin ƙaddamar da shirin tallafawa al’umma da ɗan majalisa mai wakiltar Shinkafi/Zurmi a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Bello Hassan Shinkafi, ya shirya.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

Shirin tallafin ya amfanar da mutane 2,000 ta hanyar raba motoci masu kyau, kekunan hawa, babura, injinan ɗinki da sauran kayan taimako.

 

A cikin wannan ziyara, Gwamna Lawal ya duba Cibiyar Kula da Mata da Yara (WCWC) a garin Shinkafi, wadda aka bayar domin cikakken gyara. Haka kuma, ya ziyarci Babban Asibitin na Shinkafi wanda aka gyara tare da sabunta kayan aikin sa, da kuma sabon asibitin gaggawa ‘Referral Hospital’ da ke nan a cikin garin.

 

A fadar Sarkin Shinkafi, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na aiwatar da manyan ayyuka a dukkan ƙananan hukumomin jihar.

 

Ya ce, “Mun zo Shinkafi yau domin duba muhimman ayyukan da gwamnatin mu ke gudanarwa tare da ƙaddamar da shirin tallafin ɗan majalisar tarayya, Hon. Bello Hassan Shinkafi.

 

“Mun kammala gyaran babban asibitin Shinkafi tare da samar masa da na’urori na zamani da za su taimaka wajen kula da lafiya cikin gaggawa ga al’umma.

 

“Sabon asibitin gaggawa zai zama jigo wajen inganta kiwon lafiya, ba kawai a Shinkafi ba, har ma ga dukan yankin arewacin Zamfara. Wannan zai rage wa jama’a wahalar neman kulawar likitoci.”

 

Gwamnan ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta mallaki tsohuwar makarantar Bafarawa domin mayar da ita Cibiyar Karatun Kimiyyar Lafiya ta Jami’ar Jihar Zamfara, inda ake ci gaba da aikin gyara don fara amfani da ita nan ba da jimawa ba.

 

Gwamna Lawal ya yaba wa Hon. Bello Hassan bisa irin wannan shirin taimakon al’umma, tare da kira ga sauran shugabanni da su mayar da hankali kan ci gaban ɗan adam.

 

SULAIMAN BALA IDRIS

Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara

7 ga Janairu, 2026

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Zamfara
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Zamfara
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Next Post
2027: Datti Baba-Ahmed Ya Ayana Neman Takarar Shugaban Ƙasa

2027: Datti Baba-Ahmed Ya Ayana Neman Takarar Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Zamfara

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.