Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa mai ritaya, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai sanar da sabon ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojojin Nijeriya nan ba da jimawa ba. Ya bayyana hakan ne a Abuja yayin wani taron horaswa da tallafa wa zawarawa da matan jami’an tsaro a fannin kasuwanci.
Ministan ya ce shirin na daga cikin matakan gwamnati na inganta jin daɗin Sojojin da kuma yabawa sadaukarwar da suke yi wajen kare ƙasar. Ya bayyana cewa lokacin yana Babban Hafsan Tsaro, albashin Sojoji ya tashi daga N49,000 zuwa N100,000, kuma yanzu ana ci gaba da ƙoƙarin sake ƙara shi.
Ya ƙara da cewa gwamnati ta fahimci irin ƙalubalen da Sojojin ke fuskanta a fagen daga, tare da muhimmiyar rawar da iyalansu ke takawa wajen ƙarfafa musu gwiwa. A cewarsa, ƙarfafa tattalin arziƙin iyalan jami’an tsaro na da matuƙar muhimmanci wajen gina rundunar soja mai ƙarfi.
A nasa jawabin, Darakta Janar na Hukumar SMEDAN, Charles Odii, ya bayyana cewa hukumar ta raba sama da Naira miliyan 25 ga zawarawa da matan sojoji 500 da mazajensu ke filin dafa. Ya ce tallafin wani ɓangare ne na asusun tallafawa kasuwanci na Naira biliyan 200 na gwamnatin tarayya, tare da alƙawarin ƙara tallafawa waɗanda suka yi amfani da kuɗin yadda ya kamata wajen bunƙasa kasuwancinsu.













