Game da matakan karshe na bincike mai lamba 301, kan tilasta yin kwadago da Amurka ta fitar, kakakin ma’aikatar harkokin ciniki ta kasar Sin ya bayyana a yau cewa, kasar Sin za ta ci gaba da mai da hankali, da bincikar matakan, da tabbatar da hakkinta kan batun.
A ranar 23 ga wannan wata ne ofishin wakilan Amurka game da harkokin ciniki, ya gabatar da matakan karshe bisa binciken mai lamba 301 da aka gudanar kan wasu kasashe wadanda ba su hana shigar da kayayyakin da aka samar ta hanyar kwadago na tilas ba, cewa za a kara buga musu harajin kwastam mai lamba 301.
Kasashe da yankuna 60 ciki har da kasar Sin lamarin ya shafa, inda Amurka ta ce za a kara kaso 12.5 bisa dari na harajin kwastam kan kasar Sin.Game da hakan, kakakin ya bayyana cewa, kasar Sin ba ta amince da tilastawa kowa yin kwadago ba, ta kuma kafa dokoki da ka’idojin tabbatar da kwadago bisa doka, da magance, da yaki da tilasta yin kwadago.
A daya hannun, kasar Amurka ba ta shiga yarjejeniyar hana tilasta yin kwadago ta shekarar 1930 ba, maimakon hakan ta yi amfani da wannan batu don fara yin bincike mai lamba 301, tare da kara buga harajin kwastam ga kasashen duniya, a wani mataki na cimma manufar bangare daya, da bayar da kariyar cinikayya, matakin da kasar Sin ta ki amincewa da shi. (Zainab Zhang)














