Mamban kwamitiin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS kuma shugaban majalisar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Wang Huning, ya yi kira da a inganta raya dangantakar gabobi biyu na mashigin tekun Taiwan tare da dunkule baki dayan kasar Sin cikin lumana.
Wang Huning ya bayyana haka ne a yau Asabar, yayin taro na 18 kan gabobin biyu da aka yi a lardin Fujian na gabashin kasar Sin. Da yake bayyana bangarorin biyu a matsayin kasar Sin daya tilo, Wang Huning ya yi kira da a yi adawa da ayyukan masu neman ’yancin kan Taiwan da tsoma baki daga waje, yana mai kira da a hada hannu wajen karewa da raya kasar Sin daya tilo.
Bugu da kari, ya bayyana fatan cewa mutanen bangarorin biyu, musammam matasa za su ci gaba da karfafa bayyana kansu a matsayin ’yan kasar Sin, da karfafa al’adun Sinawa da ma kasar da kanta, tare da hada hannu wajen daukaka farfado da kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post