Kungiyar dalibai ta kasa ta kafa kwamiti mai zaman kansa domin ya rika bin diddiki na yadda yadda ake tafiyar da hukumar (TETFund) a fadin manyan makarantun da suke a Nijeriya.
Ita wannan niyar kamar yadda wani bayanai mai dauke sa hannun Shugaban kungiyar na kasa Komrade, Akinteye Babatunde Afeez, bai wuce domin a tabbatar da ana aiwatar da ayyukan na Hukumar bilhakki da gaskiya da rikon amana a lokacin da ake amfani da kudin wajen yin ayyukan da za su taimaka a bangaren na ilimi.
Kungiyar ta dalibai ta ce tana bin lamarin sau da kafa irin gudunmawar da gwamnatin tarayya ta ke badawa ta hanyar Hukumar TETFund,domin kuwa an kashe biliyoyin Nairori a shekarun da suka gabata domin a samu inganta kayan more rayuwa a makaranta wadanda su ma suna taimakawa wajen yin bincike,harkar karatu da kuma yadda za ayi ta yin abubuwa sannu a hankali a manyan makarantu.
NANS ta ce zuba hannun jari a ilimi ai ana yin hakan ne domin bunkasa ilimi, ta ce shi lamarin zuba jarin an yi shi ne domin a bunkasa ita nagartar ilimin saboda daliban Nijeriya,ta haka Sadai kuma,ba ta ji dadin wasu ‘yan guna- gunin da ake yi ba na abinda ake yi akan yadda ake aiwatar da wasu daga cikin ayyukan.
Irin maganganun sai kara karuwa suke yi daga wurare daban- daban na yadda ake yin watsi da ayyukan da aka fara,ko kuma a yi shi ba tare da inganci ba, ko abin ya kasance an yi amfani ne da kayan aikin da basu dace ba, ko an yi jinkirin kammala shi aiki bayan ga yarjejeniyar da aka yi, sai kuma wata magana yadda su ‘yan kwangilar suke tafiyar da ayyukan na su, musamman ma a makarantun da suka kamata ayi masu irin wadannan ayyukan.
“Irin wadannan abubuwan dole ne su sa al’umma su rika fadar maganganu ba kai hakanan ba bu tunanin kome mutane su rika fadar wadannan maganganun, har ma wasu ma su fara tambayar ina ma amfanin kasancewar ita TETFund da taimakon da ta kan yi wurare daban- daban akan dalibai da kuma irin tsarin na ilimiin kamar dai yadda bayanin ya kasance ne,”.
Sabon kwamitin da aka kaddamar kamar yadda, kungiyar NAN ta yi bayani aikin shi, shi ne ya fara rangadi na kasa inda zai je manyan makarantu, ya tabbatar da kuma ganin yadda ayyukan taimakawa da TETFund ta bayar ayi a wane irin hali suke ciki.
Za ta iya gane wane irin aikin aka yi, amfani da wane irin kayau, nagarta shi aikin ko ayyukan, da kuma kowane irin tasiri aikin ko ayyukan za su yi ma dalibai da kuma al’ummar wurin da makarantar ta ke.
Hakanan ma kwamitin zai mika dukkan abubuwan da ya gani da kuma shawarar da ya bada cikin kwana 90 ko wata uku ke nan, bayan nan sai ita NANS za ta ce Shugabanta kadai zai iya cewa ga irin matakin da ya da ce a dauka.
Kamar dai yadda kungiyar ta ce, rahoton za a turwa fadar Shugaban kasa, tma’aikatar ilimi ta tarayya da sauran masu ruwa da tsaki domin daukar matakin da ya dace idan akjwai wani abinda ya tada kura.
NANS ta bayyana kwamitin zai kasance karkashin Shugabancin Komrade Salahudeen Lukman, tare da Gambo Abubakar wanda zai kasance matsayin Sakatare da mambobi biyar.













Discussion about this post