ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

by Sani Anwar
1 hour ago
Nijeriya

Babban Hafsan Sojan Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana cewa; haɗin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula, yana da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa.

Shaibu ya bayyana hakan ne jiya, yayin wani taron kiwon lafiya da aka gudanar a al’ummar Okrika a Jihar Ribas, a matsayin wani ɓangare na ayyukan bikin ranar sojojin Nijeriya na 2026 (NADCEL).

Babban Hafsan Sojan Ƙasa, wanda kwamandan rundunar sojojin Nijeriya, Manjo Janar Emmanuel Mustapha, ya wakilta, ya ce; lafiyar al’umma na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Bikin Ranar Sojojin Nijeriya, na ba mu dama ba kawai don tunawa da jarumtaka, sadaukarwa da nasarorin da jami’anmu na sojoji suka samu wajen kare ƙasarmu ba, har ma da ƙarfafa dangantakarmu da al’ummomin da muke yi wa hidima.

Wannan aikin kiwon lafiya, na nuna jajircewar sojojin Nijeriya ga sha’anin lafiya, walwala da wadatar al’ummar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

“Sojojin Nijeriya sun fahimci cewa, tsaro da ci gaba suna da alaƙa ta ƙut-da-ƙut. Yawan al’umma lafiyayyu, na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa da kuma ɗorewar zaman lafiya.” “Yayin da sojojinmu ke ci gaba da fuskantar rashin tsaro a wurare daban-daban na aiki, ciki har da ta’addanci, fashi da makami, sace-sacen mai, da sauran ayyukan laifuka, muna ci gaba da jajircewa wajen tallafa wa hukumomin farar hula ta hanyar shirye-shiryen agaji da na al’umma kamar haka.

“An shirya wayar da kan jama’a a yau, domin samar da shawarwari kyauta na likita, binciken ɗakin gwaje-gwaje, magani, ilimin lafiya da ayyukan tura mutane ga membobin wannan al’umma,” in ji shi.

Shugaban rundunar sojin ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa, wayar da kan jama’a ta hanyar kiwon lafiya, ba wai kawai zai magance matsalolin lafiya nan take ba ne, har ma da ƙarfafa salon rayuwa mai inganci da kuma wayar da kan jama’a game da rigakafin cututtuka.

Har ila yau, ya yaba wa Ƙaramar Hukumar Okrika, sakamakon haɗin gwiwarta, kuma ya tabbatar da cewa; rundunar sojin Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da duk masu ruwa da tsaki, don inganta zaman lafiya, tsaro da kuma ci gaba.

Babban Hafsan Sojan Ƙasa, ya kuma ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro ta hanyar samar da bayanai masu inganci da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka da kuma tabbatar da tsaron al’ummomi.

Nijeriya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’
Labarai

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
Next Post
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.