Babban Hafsan Sojan Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana cewa; haɗin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula, yana da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa.
Shaibu ya bayyana hakan ne jiya, yayin wani taron kiwon lafiya da aka gudanar a al’ummar Okrika a Jihar Ribas, a matsayin wani ɓangare na ayyukan bikin ranar sojojin Nijeriya na 2026 (NADCEL).
Babban Hafsan Sojan Ƙasa, wanda kwamandan rundunar sojojin Nijeriya, Manjo Janar Emmanuel Mustapha, ya wakilta, ya ce; lafiyar al’umma na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa.
“Bikin Ranar Sojojin Nijeriya, na ba mu dama ba kawai don tunawa da jarumtaka, sadaukarwa da nasarorin da jami’anmu na sojoji suka samu wajen kare ƙasarmu ba, har ma da ƙarfafa dangantakarmu da al’ummomin da muke yi wa hidima.
Wannan aikin kiwon lafiya, na nuna jajircewar sojojin Nijeriya ga sha’anin lafiya, walwala da wadatar al’ummar Nijeriya.
“Sojojin Nijeriya sun fahimci cewa, tsaro da ci gaba suna da alaƙa ta ƙut-da-ƙut. Yawan al’umma lafiyayyu, na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban ƙasa da kuma ɗorewar zaman lafiya.” “Yayin da sojojinmu ke ci gaba da fuskantar rashin tsaro a wurare daban-daban na aiki, ciki har da ta’addanci, fashi da makami, sace-sacen mai, da sauran ayyukan laifuka, muna ci gaba da jajircewa wajen tallafa wa hukumomin farar hula ta hanyar shirye-shiryen agaji da na al’umma kamar haka.
“An shirya wayar da kan jama’a a yau, domin samar da shawarwari kyauta na likita, binciken ɗakin gwaje-gwaje, magani, ilimin lafiya da ayyukan tura mutane ga membobin wannan al’umma,” in ji shi.
Shugaban rundunar sojin ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa, wayar da kan jama’a ta hanyar kiwon lafiya, ba wai kawai zai magance matsalolin lafiya nan take ba ne, har ma da ƙarfafa salon rayuwa mai inganci da kuma wayar da kan jama’a game da rigakafin cututtuka.
Har ila yau, ya yaba wa Ƙaramar Hukumar Okrika, sakamakon haɗin gwiwarta, kuma ya tabbatar da cewa; rundunar sojin Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da duk masu ruwa da tsaki, don inganta zaman lafiya, tsaro da kuma ci gaba.
Babban Hafsan Sojan Ƙasa, ya kuma ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro ta hanyar samar da bayanai masu inganci da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka da kuma tabbatar da tsaron al’ummomi.














