Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet), ta yi gargaɗin cewa; jihohi 27 a faɗin ƙasar nan, za su iya fuskantar ambaliyar ruwa mai ƙarfi daga tsakanin 1 ga watan Yuli zuwa 10 ga Yuli, yayin da damina ke ƙara ƙarfi.
A cikin hasashenta na barazanar ambaliyar ruwa mai ƙarfi a cikin shekaru goma na farko na watan Yuli, hukumar ta ce; ruwan sama mai ƙarfi da aka samu a watan Yuni ya bar ƙasa ta cika sosai, wanda hakan ya sa yankuna da dama suka fi fuskantar barazanar ambaliyar ruwa, sakamakon ƙarin ruwan sama.
NiMet ta bayyana cewa, ƙololuwar lokacin ruwan sama, yawanci yana farawa ne a watan Yuli, wanda ke ƙara yiwuwar afkuwar ambaliyar ruwa, musamman a yankunan da ke da ƙarancin ruwa, birane, yankunan bakin teku da kuma wuraren da tsarin magudanar ruwansu ba shi da kyau.
Jihohin da aka gano suna cikin hatsari, sun haɗa da Taraba, Sakkwato, Borno, Zamfara, Kebbi, Katsina, Kaduna, Nasarawa, Filato, Adamawa, Kwara, Kogi, Oyo, Ogun, Legas, Osun, Ekiti, Delta, Edo, Abiya, Imo, Anambira, Inugu, Akwa Ibom, Kuros Riba, Ribas da kuma Bayelsa.
Hukumar ta kuma yi gargaɗin cewa, ruwan sama mai tsanani zai iya kawo cikas ga ayyukan wutar lantarki da sadarwa a yankunan da abin ya shafa. Har ila yau, an shawarci masu ababen hawa da masu zirga-zirgar jiragen sama, da su yi taka-tsantsan sakamakon cewa; ruwan sama mai ƙarfi zai iya rage gani.
NiMet ta ƙara yin gargaɗin cewa, ambaliyar ruwa na iya lalata hanyoyi, gadoji, kayayyakin more rayuwa na magudanar ruwa da filayen noma, wanda hakan ke haifar da asarar amfanin gona. Ta kuma yi kira ga hukumomin lafiya, da su shirya don yiwuwar ƙaruwar cututtukan da ke yaɗuwa, sakamakon ambaliyar ruwa da rashin tsaftar muhalli.













