An shafe tsawon lokaci ana tafka muhawara akan shirin KADDARA mai dogon zango da kamfanin Abnur Entertainment ke shiryawa, yanzu dai an kammala ɗaukar fim ɗin amma kuma ya wuce ya bar wata ƙ
ullalliyar tambaya a zukatan masu kallo da har yanzu suka kasa samun amsarta, tambayar ita ce, ANYA ANA SAMUN IRIN WANNAN KADDARAR?, a cikin shirin da aka shafe watanni ana gutsurawa masu kallo, an ga wata mata mai suna Maimuna cikin wani irin yanayi na rashin dacewa a gidajenta na aure.
A auren Maimuna na farko dai ta haɗu da miji irin masu tsananin kishin da basu iya jure ganin wani ya raɓe ta ko da ace ɗan uwanta ne kuwa, har ta kai ga ya hanata amfani da wayarta ta hannu tareda buƙ
atar ta goge duk wani shafi da takeda shi a kafafen sada zumunta abinda ta nuna turjiya akai, daga ƙarshe dai auren Maimuna da mijinta na farko ya mutu ba tareda an cimma wata matsaya ba.
Mijinta na biyu kuwa sai aka sameshi irin mutanen nan ne da Ibada bata damesu ba, a taƙaice dai mijin Maimuna na biyu ko Sallah ba ya yi akan lokaci, watarana ma sai ya manta da yin Sallar bakiɗaya, matar tayi iyakar ƙoƙarinta wajen ganin ta dawo da mijin nata ya ci gaba da kula da Ibada amma haƙarta bata cimma ruwa ba inda har yakai ga cewa matuƙar za ta matsa mashi to za su iya rabuwa, daga ƙarshe dai haka aka yi, dole auren ya mutu.
Aure na uku da Maimuna tayi shine inda ta auri wani hamshaƙin mai kuɗi kuma ɗan boko inda suke zaune Lafiya ƙalau na tsawon lokaci ba kamar a sauren gidajen da ta fito ba, matsala ɗaya da ta fuskanta a auren mai kuɗin shi ne yadda mahaifiyar mijin nata taƙi ta goyi bayan zuwan Maimuna makaranta domin cigaba da karatunta, inda ta ce dole ne ta tsaya wajen kula da yayan mijin nata marayu da mahaifiyarsu ta rasu ta bari, ana haka kwatsam sai mutuwa ta ɗauke mijin nata.
Dagananan Maimuna ta sake wani auren, amma a wannan lokacin ba mai kuɗi tasamu ba, hasalima sabon angon ya daɗe yana roƙon Allah ya haɗa shi da wata mai abin hannunta ya yi wuf da ita, duba da cewar Maimuna ta samu yan kuɗaɗe bayan rasuwar mijinta na baya, sabon mijin nata ya yi amfani da wannan damar da ya samu yayi babakere da Dukiyar Maimuna, ba tare da la’akarin cewa Dukiyar ta marayu bace, almubazzarancin sabon mijin na daga cikin abinda ya janyo aurensu ya rabu da Maimuna
Harwayau dai KADDARAR da ke bibiyar Maimuna ba ta ƙare ba, domin kuwa aurenta na gaba kuma na biyar shi ne wanda ta auri wani bawan Allah wanda yake da lalurar da ta hana shi haɗa gado da sabuwar amaryar tashi, tunda Maimuna ta gano hakan sai ta fara kokwanton ɗorewar auren, daga ƙarshe dai haka ta faru dole auren ya mutu, domin kowa yaje ya samu daidai dashi.
Amma dai daga ƙarshe Maimuna ta samu salama a aurenta na gaba, inda ta auri ɗan uwanta wanda tunda farko masu kallo suka yi tunanin babu Aure a tsakaninsu sakamakon zamansu a Gida daya,wannan fim ɗin ya janyo wa waɗanda suka shirya shi da suka hada da Marubucin Labarin, Darakta da kuma Furodusa yabo daga masu kallon fim ɗin, inda suka ce wannan fim ɗin ya nuna yadda ake jaraba mutum, idan kuma yayi haƙuri daga ƙarshe sai ya ga ribar haƙurin.














