A kwanan nan, ma’aikatar kula da rayuwar jama’a ta kasar Sin ta mika sanarwa ga hukumomin kasar masu inganta rayuwar jama’a na matakai daban daban, inda ta bukaci da su lura sosai wajen aiwatar da matakan kandagarkin hadarin ambaliyar ruwa da ceton jama’a yadda ya kamata.
Sanarwar ta ce kamata ya yi a lura da barazanar da jama’a suke fuskanta sakamakon yiwuwar abkuwar hadarin ambaliyar ruwa a kwanaki masu zuwa, da daukar matakan kandagarki a wuraren kula da tsoffi da marayu da asibitocin masu tabin hankali don magance yiwuwar abkuwar matsaloli, da daidaita ayyukan kandagarki, da ajiye isassun kayayyakin da ake bukata yayin da ake gudanar da shirin ko-ta-kwana, a kokarin tabbatar da ganin jama’a ba su fuskanci matsalolin rayuwa ba.
A sa’i daya kuma, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, ofishin kula da aikin kandagarkin ambaliyar ruwa ya kaddamar da shirin ko-ta-kwana na matakin farko, inda ya sa jami’an hukumomi masu kula da ruwa, da gini, da aikin sufuri, da sadarwa, da aikin ceto, da rundunar sojoji da ‘yan sanda zama a waje guda don tinkarar ambaliyar ruwa tare.
Zuwa yanzu, a birnin Beijing, an kaurar da mutane 103,951 zuwa wurare masu tsaro, da rufe wuraren kula da tsoffi 73 tare da sake tsugunar da wasu dattawa 1,902, da dakatar da ayyukan wasu wuraren yawon shakatawa 188, da tsayar da ayyukan gini 3,318, da mai da cikakken hankali kan aikin tabbatar da tsaron hanyoyin da ke dab da koguna, da wadanda suka ratsa yankunan tsaunuka. (Bello Wang)














