Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta tsawaita wa’adin da ta bai wa jam’iyyun siyasa domin miƙa sunayen ’yan takararsu na zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya na shekarar 2027 da ƙarin kwanaki uku.
Hukumar ta sanar a ranar Lahadi cewa wa’adin, wanda tun da farko zai ƙare a ranar Asabar, 11 ga Yulin 2026, yanzu an tsawaita shi zuwa ƙarfe 12 na dare na ranar Talata, 14 ga Yulin 2026.
Sanarwar ta samu sa hannun Kwamishinan Hukumar kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Ilimantar da Masu Zaɓe, Mohammed Kudu Haruna.
Ya bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne bayan roƙon da kungiyar Inter-Party Advisory Council (IPAC), wanda ya nemi karin lokaci a madadin jam’iyyun siyasa da ba su samu damar ɗora sunaye da bayanan ’yan takararsu cikin wa’adin da aka kayyade ba.
A cewar INEC, tsawaita wa’adin na da nufin tabbatar da ƙarin damar shigar da dukkan jam’iyyun siyasa cikin tsarin zaɓe, tare da ci gaba da bin tanade-tanaden doka.














