Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta kama mutum shida da ake zargi da hannu a kisan wasu matafiya biyu da wasu fusatattun mutane suka yi a ƙauyen Gidan Kalu da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Yero ta jihar.
An bayyana sunayen waɗanda aka kashe da Muhammadu Sani, mai shekara 45, da Aliyu Mohammed, mai shekara 40, dukkaninsu mazauna ƙauyen Umar da ke Ƙaramar Hukumar Igabi. Rahotanni sun ce suna kan babur ne zuwa Tudun Wada, Zariya, domin duba wani ɗan uwansu mara lafiya lokacin da lamarin ya faru a ranar 1 ga Yuli, 2026.
A cewar ƴansanda, yayin da suke wucewa ta ƙauyen Gidan Kalu, kusa da Maraban Jos, wasu mazauna yankin sun yi zargin cewa su ɓarayi ne saboda sun gan su a kan sabon babur, inda suka fara ihu da cewa, “ɓarayi ne.”
Saboda tsoron kada a kai musu hari, mutanen biyu sun bar babur ɗin suka gudu. Sai dai wasu fusatattun mutane suka bi su, duk da cewa sun yi ƙoƙarin bayyana cewa ba masu laifi ba ne.
Ƴansanda sun ce har ma wasu daga cikin waɗanda suka kai harin sun san mutanen, amma duk da haka suka yi musu duka har suka mutu.
Rundunar ta ce jami’anta daga Sashen Birnin Yero sun isa wurin da gaggawa bayan samun rahoton lamarin, inda suka kama Abdullahi Mukailu Kigo da wasu mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan.
A cewar rundunar, waɗanda aka kama sun amsa rawar da suka taka a lamarin, kuma suna tsare yayin da ake ci gaba da bincike domin gano da kuma cafke sauran waɗanda suka shiga harin.
Kwamishinan Ƴansandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yi Allah wadai da abin da ya faru, yana mai bayyana kisan gilla da taron jama’a ya aikata a matsayin aikin rashin ɗa’a. Ya kuma sha alwashin gurfanar da duk wanda bincike ya nuna yana da hannu a lamarin, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
Ya gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, yana jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a abin da ake kira ɗaukar doka a hannu (jungle justice) zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.
Kwamishinan ya tunatar da jama’a cewa kotu ce za ta tabbatar da wanda bai da laifi da mai laifi, tare da ƙarfafa su da su riƙa kai rahoton waɗanda suke zargi ga ƴansanda ko sauran hukumomin tsaro domin gudanar da bincike da bin doka.
Wannan sabon lamari ya faru ne makonni kaɗan bayan da wasu fusatattun mutane suka kashe tare da ƙona Malama Ummulkhair, malamar makarantar Islamiyya, bisa zargin sata yara wanda daga baya aka tabbatar ƙarya ce. Lamarin ya faru ne a Maraban Jos, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna, a ranar 21 ga Yuni, 2026.
Rahotanni sun ce wasu mazauna yankin sun zarge ta da yunƙurin satar yara yayin da take kan hanyarta ta zuwa wani wa’azin addini a ranar Lahadi da rana.
Zargin ya bazu cikin sauri, wanda ya jawo taron jama’a suka kai mata hari kafin jami’an tsaro su ceto ta tare da kai ta ofishin ƴansanda domin kariya.
Sai dai daga baya, ɗaruruwan matasa da mazauna yankin sun kewaye ofishin ƴansandan suna neman a miƙa musu ita. Duk da ƙoƙarin jami’an tsaro na shawo kan lamarin, taron jama’ar ya rinjayi jami’an, ya fitar da ita tare da ƙona ta har lahira.
Daga bisani, Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 24 a gaban Kotun Majistare bisa zarginsu da hannu a kisan Malama Ummulkhair.
Kotun ta ba da umarnin a tsare dukkan waɗanda ake tuhuma a gidan gyaran hali har zuwa lokacin yanke hukunci, sannan ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 21 ga Yuli, 2026.













