ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
11 seconds ago
Kaduna

Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta kama mutum shida da ake zargi da hannu a kisan wasu matafiya biyu da wasu fusatattun mutane suka yi a ƙauyen Gidan Kalu da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Yero ta jihar.

An bayyana sunayen waɗanda aka kashe da Muhammadu Sani, mai shekara 45, da Aliyu Mohammed, mai shekara 40, dukkaninsu mazauna ƙauyen Umar da ke Ƙaramar Hukumar Igabi. Rahotanni sun ce suna kan babur ne zuwa Tudun Wada, Zariya, domin duba wani ɗan uwansu mara lafiya lokacin da lamarin ya faru a ranar 1 ga Yuli, 2026.

A cewar ƴansanda, yayin da suke wucewa ta ƙauyen Gidan Kalu, kusa da Maraban Jos, wasu mazauna yankin sun yi zargin cewa su ɓarayi ne saboda sun gan su a kan sabon babur, inda suka fara ihu da cewa, “ɓarayi ne.”

ADVERTISEMENT

Saboda tsoron kada a kai musu hari, mutanen biyu sun bar babur ɗin suka gudu. Sai dai wasu fusatattun mutane suka bi su, duk da cewa sun yi ƙoƙarin bayyana cewa ba masu laifi ba ne.

Ƴansanda sun ce har ma wasu daga cikin waɗanda suka kai harin sun san mutanen, amma duk da haka suka yi musu duka har suka mutu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

Rundunar ta ce jami’anta daga Sashen Birnin Yero sun isa wurin da gaggawa bayan samun rahoton lamarin, inda suka kama Abdullahi Mukailu Kigo da wasu mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan.

A cewar rundunar, waɗanda aka kama sun amsa rawar da suka taka a lamarin, kuma suna tsare yayin da ake ci gaba da bincike domin gano da kuma cafke sauran waɗanda suka shiga harin.

Kwamishinan Ƴansandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yi Allah wadai da abin da ya faru, yana mai bayyana kisan gilla da taron jama’a ya aikata a matsayin aikin rashin ɗa’a. Ya kuma sha alwashin gurfanar da duk wanda bincike ya nuna yana da hannu a lamarin, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.

Ya gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, yana jaddada cewa duk wanda aka samu da hannu a abin da ake kira ɗaukar doka a hannu (jungle justice) zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Kwamishinan ya tunatar da jama’a cewa kotu ce za ta tabbatar da wanda bai da laifi da mai laifi, tare da ƙarfafa su da su riƙa kai rahoton waɗanda suke zargi ga ƴansanda ko sauran hukumomin tsaro domin gudanar da bincike da bin doka.

Wannan sabon lamari ya faru ne makonni kaɗan bayan da wasu fusatattun mutane suka kashe tare da ƙona Malama Ummulkhair, malamar makarantar Islamiyya, bisa zargin sata yara wanda daga baya aka tabbatar ƙarya ce. Lamarin ya faru ne a Maraban Jos, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna, a ranar 21 ga Yuni, 2026.

Rahotanni sun ce wasu mazauna yankin sun zarge ta da yunƙurin satar yara yayin da take kan hanyarta ta zuwa wani wa’azin addini a ranar Lahadi da rana.

Zargin ya bazu cikin sauri, wanda ya jawo taron jama’a suka kai mata hari kafin jami’an tsaro su ceto ta tare da kai ta ofishin ƴansanda domin kariya.

Sai dai daga baya, ɗaruruwan matasa da mazauna yankin sun kewaye ofishin ƴansandan suna neman a miƙa musu ita. Duk da ƙoƙarin jami’an tsaro na shawo kan lamarin, taron jama’ar ya rinjayi jami’an, ya fitar da ita tare da ƙona ta har lahira.

Daga bisani, Rundunar Ƴansandan Jihar Kaduna ta gurfanar da mutane 24 a gaban Kotun Majistare bisa zarginsu da hannu a kisan Malama Ummulkhair.

Kotun ta ba da umarnin a tsare dukkan waɗanda ake tuhuma a gidan gyaran hali har zuwa lokacin yanke hukunci, sannan ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 21 ga Yuli, 2026.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026

LABARAI MASU NASABA

‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.