ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

by Sani Anwar
36 minutes ago
Naira

Ƙungiyar Ma’aikatan Tarayya (FWF), ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta biyan haƙƙoƙin ma’aikatan da ke wannan ƙasa, ta aiwatar da mafi ƙarancin albashi na ƙasa na naira 300,000, sannan ta magance abin da ta bayyana a matsayin mafi muni a cibiyoyin gyaran hali na ƙasar.

Mai kula da harkokin ƙungiyar na ƙasa, Mista Andrew Emelieze, ya gabatar da buƙatun a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Emelieze, ya yi kira ga gwamnati da ta biya bashin albashin watanni biyu da ke kan ma’aikatan tarayya, tun daga watan Yunin 2024, ta biya bashin kashi 40 cikin 100 na alawus na musamman, sannan ta biya dukkanin basussukan ma’aikatan tarayya, waɗanda aka aiwatar na sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa na naira 70,000.

ADVERTISEMENT

“Muna tunatar da gwamnatin tarayya nauyin da ke kanta na ma’aikatan tarayya, gami da albashin wata biyu, bashin alawus na musamman da kuma cikakken aiwatar da mafi ƙarancin albashi na 70,000,” in ji shi.

Mai kula da harkokin ƙungiyar, ya kuma buƙaci Shugaba Bola Tinubu, da ya yi gaggawar yin bitar albashin ma’aikata, yana mai jayayya cewa; albashin da ake samu a yanzu, bai isa ya maye gurbin hauhawar farashin kayayyaki ba.

LABARAI MASU NASABA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

“Muna sake nanata shawararmu ta mafi ƙarancin albashi na 300,000 da matsakaicin albashi na naira miliyan 1.5 ga ma’aikatan da ke mataki na 17. Muna jiran amsa nan take daga Mista Shugaban Ƙasa,” in ji shi.

Bayan walwalar ma’aikata, Emelieze ya nuna damuwa kan yanayin jami’an gyaran hali, yana zargin cewa; an tilasta wa mutane da yawa sayen kayan aiki na hukuma da suka haɗa da takalma, bel, tambarin matsayi da sauran kayan aiki tare da kuɗaɗensu.

Ya kuma yi zargin cewa, jami’an da ke zaman jarrabawar ƙarin girma, sun ba da gudummawar kuɗi don jin daɗin masu jarrabawar, yana mai ƙarawa da cewa; an ruwaito cewa, irin waɗannan ayyuka sun kasance a cikin Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya.

“Muna kira da a gudanar da bincike mai zurfi, kan zarge-zargen cin hanci, yayin atisayen ƙarin girma, kuma muna buƙatar inganta jin daɗin jami’an gyaran hali da sauran ma’aikatan tsaro,” in ji shi.

Naira
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe

MASU ALAKA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.