Yau Laraba, ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda yayin zaman, wani dan jarida ya yi tambaya game da rashin gamsuwar Amurka da kasafin sayen makamai na yankin Taiwan.
Game da hakan, kakakin ofishin Zhang Han, ta jaddada cewa batun Taiwan na harkokin cikin gida na kasar Sin ne, kuma ba a amince wani sashe na waje ya tsoma baki cikinsa ba.
Sin na adawa da duk wani nau’in hadin gwiwar soji tsakanin Amurka da yankin Taiwan na kasar Sin. Ya ce mun bukaci Amurka da ta rike ka’idar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”, da takardu guda 3 da bangarorin biyu suka cimma matsaya kansu dangane da huldar Sin da Amurka, ta kuma yi taka-tsantsan wajen magance batun Taiwan, ta daina sayarwa Taiwan makamai, kana ta kauracewa aikewa da sakon kuskure ga ’yan awaren Taiwan. (Amina Xu)















Discussion about this post