Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a Jihar Kwara domin ƙarfafa tsaro da kuma yaƙi da ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata munanan laifuka.
Za a kafa bataliyar ne a garin Omu Aran, hedikwatar ƙaramar hukumar Irepodun, kuma ana sa ran hakan zai ƙara yawan sojojin da za a tura yankin tare da ƙarfafa ayyukan soji, musamman a wuraren da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga da garkuwa da mutane.
Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da Mataimakin Babban Sakataren Yaɗa Labaransa, Mashood Agboola, ya fitar a ranar Talata.
Gwamnan ya ce amincewar da Shugaba Tinubu ya bayar wani ƙarin tabbaci ne na ƙudurin Gwamnatin Tarayya na magance matsalolin tsaro da ke addabar jihar.














