Ƙungiyar Kwankwasiyya ta musanta iƙirarin Shugaban Jam’iyyar PRP, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, cewa Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi sun tattauna da jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.
Baba-Ahmed ya bayyana hakan a wani shirin siyasa na Hausa a DITV a Kaduna cewa tattaunawar da aka yi tsakanin PRP da jagororin adawar biyu ta rushe ne saboda rashin jituwa kan sharuɗan shiga jam’iyyar.
Ya yi zargin cewa Kwankwaso da Obi sun nemi tabbacin samun tikitin takarar shugaban ƙasa ba tare da hamayya ba.
Sai dai mai magana da yawun Kwankwasiyya, Dakta Habibu Sale, ya ƙaryata batun, yana mai cewa babu wata ganawa ko tattaunawa a hukumance tsakanin Kwankwaso, Obi da shugabannin PRP.
Ya ce PRP kamar wasu jam’iyyun adawa, ta yi ƙoƙarin tuntuɓar wasu ƙungiyoyin siyasa yayin rikice-rikicen da ke tsakanin jam’iyyun adawa, amma ya ce hakan bai kai ga wata tattaunawa a hukumance ba ko neman tikitin takara ba.
Sale ya kuma bayyana kalaman Baba-Ahmed a matsayin yunƙurin jan hankalin jama’a, yana mai cewa PRP ba ta da tasiri a siyasa da zai sa manyan ’yan adawa irin su Kwankwaso da Obi su nemi irin waɗannan sharuɗa.















Discussion about this post