ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

by Sulaiman
2 hours ago
Makarantu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sanya hannu kan wasu Dokokin Zartarwa da za su kafa sabon tsarin gudanar da harkokin ilimi a jihar, tare da ƙaddamar da rabon Manhajar Karatu ta Ƙasa ga makarantun gwamnati.

Gwamnan ya ƙaddamar da shirin ne a ranar Talata yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi da aka gudanar a Gidan Gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau.A cikin wata sanarwa da Mai Magana da Yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa dokokin zartarwar sun ƙunshi sabbin tsare-tsaren gudanar da harkokin kuɗaɗen ilimi, kare makarantu, tantance nau’o’in makarantu, tabbatar da ingancin ilimi, kula da lafiyar ɗalibai da kuma inganta tsaro a makarantu.

Makarantu

Sanarwar ta ce, gyare-gyaren sun kuma shafi yadda za a gudanar da makarantu, tsarin ciyar da ɗalibai, walwalar ɗalibai, tabbatar da tsaron zirga-zirgar makaranta, aiwatar da shirin Makarantu Masu Tsaro (Safe Schools Initiative) da kuma tsara yadda ake gudanar da bukukuwan kammala karatu.Bugu da ƙari, gwamnatin ta kuma gabatar da sauye-sauye da suka haɗa da gudanar da jarrabawa a tsari guda, inganta ayyukan kula da lafiyar makarantu, naɗin shugabannin makarantu bisa cancanta, bunƙasa ilimin bai ɗaya, da kuma ƙarfafa koyar da Kimiyya, Fasaha, Injiniyanci da Lissafi (STEM), Ilimin Fasaha da Sana’o’i (TVET) da ilimin zamani na fasahar dijital.Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa ilimi ya fi kasancewa kawai wata hidimar zamantakewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce ilimi shi ne mafi ƙarfi wajen rage talauci, samar da zaman lafiya, ƙarfafa tsaro, haɓaka tattalin arziki da kuma shirya matasa domin fuskantar ƙalubalen duniya mai dogaro da ilimi.“A yau muna mayar da wannan ƙuduri zuwa matakan da za su ɗore ta hanyar sanya hannu da kuma ƙaddamar da waɗannan Dokokin Zartarwa.“Waɗannan dokoki ba umarni ne daban-daban ba. Tsarin mulki ne cikakke da aka tsara domin inganta tafiyar da makarantu, ƙarfafa riƙon amana, kare kadarorin ilimi na gwamnati, inganta yadda ake samar da kuɗaɗen ilimi, tabbatar da tsaro, ɗaga darajar ilimi, inganta sakamakon karatu da kuma shirya yaranmu domin ƙarni na 21,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, tsawon shekaru an fi mayar da hankali wajen gina azuzuwa da dakunan gwaje-gwaje, amma ƙwarewa ta nuna cewa gine-gine kaɗai ba su wadatar wajen samar da ingantaccen ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

Gwamnatin Kano Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi

Makarantu

Tun da farko, Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Zamfara, Abdulmalik Abubakar Gajam, ya ce nasarar kowace manhajar gyaran ilimi na dogara ne da haɗin gwiwar gwamnati, malamai, iyaye, al’umma, sarakunan gargajiya, abokan hulɗar ci gaba da kuma masu zaman kansu.

Ya bayyana cewa manufar waɗannan gyare-gyare ita ce tabbatar da makarantu masu tsaro, ingantaccen shugabanci, lafiyar ɗalibai, kyakkyawan koyarwa, sakamako mai inganci a fannin ilimi da kuma ƙara yawan amincewar jama’a da tsarin ilimin jihar.

Makarantu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026
  • Sulaiman
    Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC
  • Sulaiman
    Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang
Labarai

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

July 22, 2026
Kano
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi

July 22, 2026
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano
Labarai

Uba Da ‘Yarsa Sun Mutu Bayan Faɗawa Rijiya A Kano

July 22, 2026
Next Post
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

LABARAI MASU NASABA

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026
Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

July 22, 2026
Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

July 22, 2026
An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

July 22, 2026
Kano

Gwamnatin Kano Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi

July 22, 2026
Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

July 22, 2026
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Uba Da ‘Yarsa Sun Mutu Bayan Faɗawa Rijiya A Kano

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.