Wata kungiyar attajirai da Amit Bhatia – attajiri dan kasar Indiya ke jagoranta, ta nuna sha’awar siyan kaso 30 na kungiyar kwallon kafa ta Liverpool dake buga gasar Premier League na kasar Ingila.
Bhatia, surukin hamshakin attajirin kasar Indiya Lakshmi Mittal, ya kasance darakta a kungiyar QPR na tsawon shekaru 18, inda ya sauka daga shugabancin kungiyar a ranar Talata.
A cikin wata sanarwa, masu rike da hannun jarin Liverpool wadanda ake yiwa lakabi da Fenway Sports Group (FSG) sun shaida wa BBC Sport cewa, “Wata kungiyar saka hannun jari da Amit Bhatia ke jagoranta ta nuna sha’awar saka hannun jari a kungiyar kwallon kafa ta Liverpool”.
Amma kuma BBC Sport ta ruwaito cewa har yanzu ba a kammala yarjejeniya da FSG ba. A shekarar 2010 FSG ta sayi Liverpool akan kudi fam miliyan 300, amma yanzu a cewar jaridar Financial Times yarjejeniyar da zasu kulla da kungiyar Bhatia na sayar da kaso 30 na Liverpool na iya kaiwa dala biliyan 6 (£4.5bn).














