Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed, da takwaransa na kasar Gedion Timothewos jiya Alhamis a birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar ta Habasha, inda dukkaninsu suka sha alwashin hada karfi, wajen ingiza aiwatar da sakamakon taron dandalin raya hadin gwiwar Sin da Afirka ko FOCAC, wanda ya gudana a birnin Beijing a shekarar 2024.
Wata sanarwar hadin gwiwa da aka rabawa manema labarai game da hakan, ta ce sassan biyu sun amince su kara zurfafa hadin gwiwa a dukkanin fannoni, tare da kara azamar gina kawancen Sin da Habasha bisa manyan tsare-tsare, a matsayin wani salo na gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya daga dukkanin fannoni a sabon zamani.
Kazalika, sassan biyu sun alkawarta zurfafa hadin gwiwa a fannonin raya al’adu, ciki har da bunkasa tattalin arziki, da cinikayya, da samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da sufuri, da fannin shari’a, tare da cin gajiyar damammakin hadin gwiwa a sabbin bangarori, irinsu cinikayyar dijital, da raya tattalin arzikin dijital, da kirkirarriyar basira, da makamashi mara dumama yanayi, da fadada hadin gwiwa a fannin al’adu da yawon bude ido, da watsa labarai, da ilimi, da cin gajiyar basirar kwararru.
Dukkanin bangarorin sun kuma jaddada aniyarsu ta daukar shekarar musayar al’ummun Sin da Afirka ta 2026, a matsayin damar ingiza musayar jama’a, da yaukaka kusanci ta hanyar al’adu da basirar al’ummunsu.
Har ila yau, sun shirya karfafa dabarun daidaita tsare-tsare da manufofin samar da ci gabansu, da zurfafa musaya a fannin kwarewar jagoranci, da hada karfi waje guda, kan turbarsu ta zamanantar da kai. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post