Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, ya ce Sin na maraba da kamfanonin waje ciki har da kamfanin Warburg Pincus, da masu zuba jari na dogon lokaci, da su ci gaba da fadada zuba jarinsu a Sin da zurfafa hadin gwiwar cimma moriya tare da Sin.
He, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya yi kiran ne yayin zantawarsa da tsohon sakataren baitul-malin Amurka Timothy Geithner, wanda a yanzu shi ne shugaban kamfanin Warburg Pincus mai hada-hadar zuba jari.
He Lifeng, ya ce Sin na aiwatar da cikakkun ka’idojin gudanarwa da aka tsara, yayin cikakken zama na hudu na kwamitin kolin JKS na 20, daidai da shawarwari da tsare-tsaren da aka tanada, karkashin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15, da ingiza gina kasuwar kasa ta bai daya, da fadada bude kofa bisa matsayin koli, da yaukaka bunkasar tattalin arziki bisa babban matsayi.
A nasa bangare, Geithner ya ce yana da kwarin gwiwa game da makomar bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, kuma kamfanin Warburg Pincus a shirye yake ya ci gaba da zurfafa shiga kasuwar kasar Sin, da ingiza nasarar hadin gwiwar raya tattalin arziki da cinikayya tsakanin Amurka da Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post