Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta bukaci Amurka ta dakatar da kangiya da takunkumai da duk wani nau’i na matsin lamba nan take kan Cuba.
Kakakin ma’aikatar ne ya bayyana haka a martaninsa ga matakin Amurka na kakaba takunkumai kan Cuba. Cuba ta ce matakan matsi da ba su dace ba da Amurka ke dauka ba su dace ba.
Kakakin ya ce, tsaurara takunkumai mara dacewa da Amurka ita kadai ke kakaba wa Cuba, sun yi matukar take hakkokin mutanen Cuba na rayuwa da samun ci gaba, tare da take ka’idojin dangantakar kasa da kasa.
A cewarsa, kasar Sin na mara baya ga Cuba ta kare tsaro da ‘yancinta, kuma tana adawa da tsoma baki cikin harkokin gidan Cuba. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post