Kasar Sin ta ce ayyukan da hukumomi masu ruwa da tsaki na kasar suka yi a yankin ruwan da ke gabas da Tsibirin Taiwan, dukkansu halaltattu ne kuma ba su da wani aibu.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ne ya bayyana haka a yau Litinin, inda ya ce kasar na da yankin raya tattalin arziki na musamman da ke karkashin cikakken ikonta da kuma bangaren yankinta da ke karkashin ruwan da ke gabas da Tsibirin Taiwan.
Ya ce tsallake kasar Sin da kaddamar da abun da ake kira wai tattaunawar shata iyaka a cikin teku da Japan da Philippines suka yi, ya keta dokokin kasa da kasa ciki har da yarjejeniyar MDD kan dokar teku da ma tushen ka’idojin huldar kasa da kasa.
Haka kuma matakan nasu sun yi matukar keta muradu da hakkokin Sin na teku, lamarin da kakakin ya ce, kasarsa ba za ta lamunta ba. (Fa’iza Mustapha)














