Tsohon gwamnan Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin “tsuntsun siyasa” da ke sauka a duk inda ya ga dama.
Ganduje ya yi wannan furuci ne yayin da yake magana kan yawaitar sauya jam’iyya da Kwankwaso ke yi, yana mai cewa hakan na nuna rashin tsayayyen matsayi a siyasa.
Ganduje, Ya ƙara da cewa sauya sheƙar da Kwankwaso ke yi daga jam’iyya zuwa jam’iyya da komawarsa daga ADC zuwa wata sabuwar Jam’iyya ba zai zama barazana ga jam’iyyar APC ba.
A cewarsa, irin wannan salon siyasa na “tashi daga wannan waje zuwa wani” na nuna raguwar ƙarfi a siyasa, yana mai jaddada cewa APC na da ƙarfi a yanzu fiye da kowane lokaci.
Wannan kalamai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa da sauya jam’iyya tsakanin manyan ‘yan siyasa gabanin zaɓen 2027.















Discussion about this post