Wasu da ake zargin ‘yan ta’addan Boko Haram ko na kungiyar ISWAP ne, sun kai hari a Makarantar Sakandare ta Gwamnati, Lassa da ke Lassa a ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno, inda suka sace ɗalibai masu yawa da ba a tantance adadinsu ba waɗanda ke rubuta jarabawar NECO.
Rahotanni sun ce maharan sun mamaye makarantar ne da misalin ƙarfe 9 na safe, inda suka riƙa harbe-harbe a iska, lamarin da ya jefa ɗalibai da malamai cikin firgici kafin su tafi da wasu daga cikin ɗaliban zuwa cikin daji.
Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Jihar Borno, Nahum Daso, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa har yanzu akwai ɗalibai da dama da ba a gano inda suke ba bayan harin.
“Da misalin ƙarfe 9 na safe ne wasu ‘yan ta’adda suka kai hari a makarantar sakandare inda suka yi ta harbe-harbe a iska. A yayin harin, an sace wasu ɗalibai da ba a tantance adadinsu ba, yayin da wasu kuma har yanzu ba a san inda suke ba,” in ji shi.
Sai dai jami’in ya ce rundunar ba ta iya tabbatar da rahotannin da ke cewa an kashe wani malami a lokacin harin ba.
Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun fara wani haɗaɗɗen samame da aikin ceto domin kubutar da ɗaliban da aka sace tare da kamo waɗanda suka kai harin.














